ALLURA CIKIN RUWA BOOK 1 CHAPTER 29 BY BILKISU S. AHMAD FUNTUA

ALLURA CIKIN RUWA BOOK 1 CHAPTER 29 BY BILKISU S. AHMAD FUNTUA

 

 

Mu duka ‘yan zafi ne a wajen harkar karatu,

saboda haka sai mu kashe lokaci mai tsawo muna

yiwa juna matashiya. Misali a nan, a kowane darasi za a sanya daya daga cikinmu ta karanta, sannan tayi bayani a kan abin da ta karanta da yadda ta fahimci. abin. Bayan ta gama sai kowace daga cikinmu ta kara bayani ko ta tambayi abin da ba ta gane ba, sai mun tabbatar kowacce daga cikinmu ta gane sannan

mu wuce wannan darasi mu shiga wani sabo.

Ta,irin wannan: hanyar muka cimma burinmu,

ba‹mu taba yadda: mu zauna, muna, zurara karatu ba tareda Fahimtar komai a ciki ba

Acikin-wannan sito da muka mai da shi

dakin mabuyar-karatu, mun Kawala shi da abubuwan da sukan-taimakamana a ashen fannin karatunmu, Na aiki wata „mata mai daikin abincin makarahtarmu wadda ke zuwa daga cikin gari, kuma gidansu baya da nisanzuwa gidanmu, ta amso, mini sabon tulu muka ajeshi a wannan sito sbd mu dinga shan ruwa ba tare da saimun tashi munje nema a wani wuri ba  haka ta amso amso mana tabarmi guda biyu, bayan

tebur da kujeru da mukasanya, idan mun gaji bisa

kujera mu kan kwanta bisa tabarma mu ci gaba da nazarin karatunmu, Sannan kuma mun yi amfani da loka din dake jikin teburanmu  don aje abincimu.kamar su biskit da cakulet da konfeles da dai yan abubuwan Tsotse-tsotsen motsa baki.

A daidai bangon da kowace daga cikinmu ke

zaune bisa kujerar kavalunlu ta lika jadawali da ke

nuna lokutan jarrabawarta. Daga nan muke dage

dantse, muka ci gaba da karatu ba ji ba gani, muka yi shiri sosai don tarbar jarrabawar mock ta share fage ga babbar jarrabawar fita,

A wannan lokaci ba mu da komi daga karatu

sai nafiloli muna neman sa’a daga wajen

Ubangijinmu. Muna cikin haka time-table ya fito na jarrabawarmu ta mock, jarrabawar ta farko da za mu fara yi ita ce ta fannin Tarihi

Muka shiga aji muka zazzauna, bayan an bamu takardun tambayoyin kowace ta dukufa wajen

duba abin da aka tambaya. Da na gama karantawa sai na daga kai na dubi Rabi ‘yar mutan Karmiya nayi mata murmushi.

Abin da yasa na juya na dube ta shi ne, daga

tambaya ta daya har zuwa ta uku ita ce ta yi mana bayaninsu. Sannan nayi musu tambaya a kan bayanin da ta bayar, to cikin ikon Allah sai gasu su ne a farko, sauran kuma mun san su kamar yunwar cikinmu. Haka muka rinka samun kowace jarrabawa cikin sauki. Idan ka ji daliba tace, jarrabawa ba ta yi wuya ba, to ta san abin da ta taka. Ko da yake ba a cewa babu wuya, sai dai a ce an riga an sha wuya wajen yawaita bitar da muka yi, idan anzo wajen jarrabawa sai mutum ya sami komi kamar wasa

Bayan mun gama jarrabawa da kwana uku aka bamu hutu na sati biyu kacal, a inda muka isa gida da ramuwar barci a kanmu. Ranar da muka sami kwana hiyu da zuwa hutu

sai ga su hajaru da direban gidan su Mama Inki sun zo tafiya da ni Kaduna, a nan muka yi tayin ta dasu, a inda na nuna musu gaskiya su yi hakuri ba zan sami zuwa ba saboda akwai karatu

a tattare dani, musamman ga shi da mun koma makaranta da sati shida zamu fara jarrabawa ta fita.Suka matsa wa mahaifina ya tura ni in tafi, sai

yace Su yi hakuri ran da na gama jarrahawa insha

Allah suna gani na Da Kyar dai suka hakura dirceba ya mai da su Kaduna.

Lokacin da muka sami kwana hudu da samun

hutu sai muka fara zuwa aikin karatu na cikin gari.

Ba ni mantawa ranar wata Alhamis da la’asar

sakaliya zamu je Reading room karatu da ni da

Hadiza, mun kusa isa ke nan sai muka hadu da wani mutum a cikin mota Marsandi mai kirar kulba, kalar ta fara ce sol. Ya sha gabanmu amma muka Ki yarda mu tsaya har muka is dakin karatu muka shiga. Mun sauna ke nan sai ga shi ya shigo, yana sanye da riga yar shara da dogon wando na farar shadda. Mutumin dai dogo ne baki mai kyan Kira, yana da dogon hanci da idanuwa wadanda su ba kanana ba

kuma basu da girma ba, kadaran-kadahan.

A tsakanin hancinsa da labbansa na sama akwai gashi wanda ya yiwa hancin nasa tsari.

Ya sami kujera ya zauna kusa damu yace

“Haba yanmata ana yi muku magana amma kun ki ku tsya? Duk wanda ya ga shigar da kukayi yasan Yanmata ne ba matan aure ba, saboda haka ai ya yan manya ba a san su da raina mutane ba” Sai Hadiza tace Yanzu Alhaji wan irin raini muka yi maka? Mu tsaya muna magana da kai bisa titi, ina ganin ai ba mutuncinka ba ne, haka mu ma ba mutuncinmu ba ne

Ya yi ajiyar zuciya ya ce,Lalle yaran nan

kuna da kaifin hankali, kin san namiji idan ya ga mace yana, so bai damu da ya tsaya a gaban ko wane ne ya yi mata magana ba. A kan yi haka ne gudun kada ta bace masa, bai sani ba ko ya sake ganin ta ko ba zai sake saduwa da ita ba, inda kuka fi mu ke nan ku mata kun iya kannewa, ku jere ko mene ne a zuciyarku”Ya dube ni ya yi murmushi, cikin ikon Allah ban san yadda

Akai na maida masa Da martanin

murmushinsa. Ba Nan da nan sai ya ji dadì, ya gyara zama ya dubi Hadiza yace

‘Ina sunan malamar?

Hmmm LABARI fa nata Tafiya shin KOYA ZATACI GABA da KAYAWA KUDAI KUCI GABA da kasancewa damu A koda Yaushe

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button

You cannot copy content of this page

Adblock Detected

YOU ARE USING ADBLOCK TURN IT OFF TO COUNTIUE BROWSING OUR WEBSITE