ARNE CHAPTER 1 BY Surayyah.M.S

ARNE CHAPTER 1 BY Surayyah.M.S

 

 

 

Cikin sanyin Daren damina ga duhun hanya,tafe suke wajen karfe 2saura na dare,alhaji abdullhi da drivern sa Musa

A daidai hanyar da yabi Jos zuwa abuja,

Dan sassauta tukin  motar yayi domin hasken touchlight da aka buga akan idanunsa

Innalillhi wa inna ilaihi rajiun,Alhaji bar….aayi

Park,park park akace musu,nan Musa agigice ya kashe motar kusa da wata bus din kasuwa da aka faffasata da harsashi

Cillo su waje sukayi ,suna binsu da naushi

Lie down flat, don’t raise ur head or I will shoot,.

‘Bari kawae suke Kansu akasa….kimanun su shida ne sun rufe furkansu da mask

Daya daga cikin ya tukare Musa bayan yagama duba shi baisami komai ba,

Nan ya masa lilis,sai da ya ga baya numfashi,

Alhji kuwa hatta agogan sa da takalmansa sanda suka cire…..

Abun mamaki shine..duk da hakan .su biyu ne suka tsaya kansa inbanda jibgarsa ba abunda sukeyi,

In banda Azaba da radadi ba abunda alhji abdullhi ke Sha,

Daga bisani dayan ya kwada masa gindin bindiga a kai,nan jini ya fara zubowa tare da jiri dake nemar kwantr da shi

Oga yakamata amasa aiki lokaci na tafiya,

Daga hannu ,yayi ma wani shakiki acikinsu,da tuntuni a tsaye yake bai motsa ba

Alaman ya harbe alhaji abdullhi su kauce

Nan ya fara karasowa,

Dan Allah kumin rai,na rokeku

alhji da ya kusa fita cikin hankalinsa  yake furtawa zan Baku dukkan abunda kuke so

Shut up, waya gaya maka Yau zallan sata muka fito,

Bushewa yayi da dariya yace Kowa xai mutu ,dole kaima ka mutu

domin gwmnatin ku ta kashe mana ogan mu dan uwan mu

Nan ya cahkamo alhaji,yace duba chan yana maida kallonsa kan motar haya wanda ba mai rai acikinsu

Said wani yaro da baiwuce shekara 13 ba makale da gawan iyayensa yana shesshekar kuka

Innalillahi wa enna ilaihi rajiun,hasbunaAllah wa neemal wakeel

Dariya suka bushe dashi dukkansu suna wani ihun cike da rashin imani…

Gunner finish him,nan ya danna harsashin zai buga kan alhaji

Ji yayi an chukwikuyesa anrike rigarsa

Ka kashe ni ka barshi,

Ni yakamata ka kashe,zan bi su mama

Banida amfani ka kasheni

Wani wawan mari ya sake masa wanda saida ya gigice

Ahakan yaron ya sake yunkurowa ya damke rigarsa sanda ya yaga  gefe daya

Nan faffadan kirjinsa wanda ya ji zanen tattoo na kan biri(monkey) yA bayyana

A fusace ya danna bindiga kan yaron zai buga

Stop gunner don’t shoot him,kill d man

Karar siren din sojoji ne suka faraji,da sauri drivernsu ya fito da motarsu a jejin

nan suka fara yunkurin tatarawa

Gunner kuwa danna bindiga yayi setin kan alhaji ya danna kat

Ihun yaron ne ya farkar da alhaji da tuni yagama sallamewa idonsa a rufe yana faman Kalmar shahada

Jini ne ya mamaye kafadan yaron, kwance a jikin alhaji ji yayi yace Jesus save me,kafin nan ya rufe idonsa sumamme,

Karasowar sojojin ke da wuya aka dura su alhaji ambulance aka fara basu taimakon gaggawa ,ba a tsaya ko ena ba sai babban asibitin abuja,

Nan aka wuce da yaron nan theatre .

Su alhaji da Musa kuma aka kaisu emergency room.

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button

You cannot copy content of this page

Adblock Detected

YOU ARE USING ADBLOCK TURN IT OFF TO COUNTIUE BROWSING OUR WEBSITE