BARIKI NA FITO CHAPTER 10
BARIKI NA FITO
CHAPTER 10
Washe gari Yarima Aliyu ne cikin shiri mota ya shiga dan dawowa garin kaduna, fita sukai daka cikin masarautar suna fita saiga Gimbiya zinatu ta kirashi d’auka yayi yace hello, tace Yarima Ina hangoku kuka fita dan Allah ka tsaya muyi sallama, yace kiyi hakuri in muka karasa za muyi waya, inna fito bana komawa, babu yanda ta iya dole hakura tayi, Yarima Aliyu sun Kai garin kaduna wajan karfe 11 da wani abu na safe, direct maraban jos suka nufa inda suka shiga cikin anguwar basu karasa gidan ba Yarima yaga habib yana tafiya yana rangwada, yarima yace ma driver dinshi tsaya da motar, bayan driver din Yarima ya tsaya yasa sauran motocin suka tsaya tunda suka shigo anguwar idon mutane ke kansu, yarima ya nuna ma driver dinshi habib yace ka kira min shi, driver din ya fita tare da fad’in angama ranka ya dad’e …..
Driver din direct wajan habib ya nufa yace bawan
Allah Yarima na son ganinka.
Habib waige ya farayi yaga dawa mutumin yake magana dan yaji yace Kai ba ke ba, habib yace
dawa kake? Mutumin yace dakai mana, yarima ke magana,
Habib yace dakata Aiba namiji ka gani a gabanka ba, mace ce a gabanka kalleni dakyau ko Kaga na
maka kama da namiji?
Driver din Yarima yace ikon Allah, kai yanzu kana gansamemen kato ka dinga kiran kanka da mace?
Habib yace dalla Mlm dakata Wlh sai in rufe idona
in sharta maka rashin mutunci.
Ganin haka driverdin yace a’ah Allah ya baki hakuri ij, yarima na son ganinki,
Shuru habib yayi yace wani yarima?
Nuna Mai motar driver din yayi tare da fad’in yana
cikin mota.
Habib yace oh dama tare kuke Aida kamin bayani
tun Farko muje.
Yarima duk wannan abunda suke yana kallonsu amma baya jin abunda suke fad’a, danko bai tambaya ba yasan habib dan daudu ne domin yanda yaga yana abu, sannan kan Yarima ya fara kullewa domin ganin irin mutanan dake sintiri a
wajan.,
Toh miye tsakanin yarinyar daya gani da wannan dan daudu din?
Jin bude motaryasa Yarima ya dawo daka duniyar tunanin daya Fara.
Habib ne ya shigo motar sanyin AC ya dukeshi ga kamshi na tashi, yace oh aljannar duniya Mai kudi bai kwana da haushin kowa ba.
Kallon Yarima yayi wanda yaga ya mishi kwarjini, yace ranka ya dade barka da zuwa, ina fatan dai
lafiya?
Yarima Aliyu yace lafiya, ina da tambayan da nake
son maka ne.
Habib kasa cewa komai yayi duk da yarima yace
mishi Kai ba ke ba, sai fadi yayi lnaji.
Yarima Aliyu yace kwanakin baya nazo wucewa na
ganka tsaye kaida wata yarinya tasa hijab a bakin
titi….
Tun Kafin Yarima ya karasa magana habib yace bariki kake nufi?
Yarima yace what bariki kaman ya?
Ganin yanda Yarima ya shiga da yaji yace bariki yasa ya gane badan hannu bane, saiya wayince yace Ina nufin gidan duniya kaman bariki ne zaka ga mutane da yawa sai yasa nace bariki kake nufi ina nufin ni inada mutane Kala Kala.
Jin haka yasa Yarima hankalinshi ya kwanta dan da haryaji kirjinshi ya fara bugawa da karfi
Yace baiyi sati biyu ba na ganka kaida wata tasa hijab ta ri’ke akwati daka gani bakuwa ce.
Habib yace au kodai Zainab kake nufi? Tasa hijab blue koh?
Yarima yace eh itace
Habib yace Zainab baiwar Allah Aiba a nan take ba, gidansu yana cikin gari, tana zuwa wajan yan
uwanta ne a nan. Yarima yace ko zaka iya kaimu gidansu?Habib yace Kai Anya zata kulaka kuwa?
lnaga ka bani number dinka inna mata magana sai in tura maka numberdinta, sai ku Fara magana koh?
Yarima yace hakan yayi bashi card dinshi yayi tare da dauko kud’i bandir d’aya y’an dubu d’aya d’aya ya bashi dubu d’ari kenan.
Habib amsa yayi tare da zabga Mai godiya yace saikajini ranka ya dade.
Kai yarima ya d’aga tare da fad’in ka tsaya a baka babban riga, inka fita kama driver dina magana.
Habib sai murna yake tare da godiya.
Habib fita yayi ya Kalli driver din Yarima, tare da Galla Mai harara yace ana magana dakai.
Driver din bud’e motaryayi
Ban San mai yarima yace Mai ba sai gashi ya rufe motartare da bud’e booth din motar da wasu fadawa ke ciki ya d’auko kaya a Leda ya mi’ka ma habib tare da fad’in gashi ij.
Habib amsa yayi tare da fad’in dan rainin wayau.
Murmushi driver din yayi tare da fad’in Allah ya
shirya, mota ya Shiga suka wuce.
Shiko habib gidan ya koma, cikin murna, direct
d’akin bariki ya nufa.
Nocking yayi tace Waye?
Yace bud’e mana.
Jin muryan habib yasa ta bud’e kofar.
Shiga yayi yana fad’in bariki bariki gskya inda ban sanki ba, da Nayi Asara.
Kallonshi tayi tace maiya faru haka? Wannan ledan fah?
Dariya yayi tare da fad’in kyauta aka ban duk saboda ke.
Tace ni? Waya baka?
Zama yayi tare da ajiye ledaryace d’an Sarkin
Zazzau Yarima, shida kanshi yazo nemanki. Tace kaman ya?
Labarin abunda ya faru ya bata, tare da fad’in Kinga kyautar da yamin ya nuna mata kud’in da Yarima ya bashi, tare da bud’e ledar shadda ce dinkakku har Kala biyu kuma duka gezna, habib
yace oh Kinga Abun arziki, ni Ina mace anban
kayan y’an maza. ‘
Bariki dariya tayi tare da fad’in wato shi ustaziya yake so? Dariya ta kuma saki oh hijab ya gani shi‘ dole yaga Kamila matar aure, dariya take Sosai harda hawaye lallai sai yanzu na gane maganan nan da ake cewa karka taba shaidan mutum domin baka san maike zuciyarsa ba, lallai inda yasan
wacece ni da bai kawo kanshi ba.
Habib yace Kedai kina da matsala kin ganshi ne? Wlh ya had’u na tabbata irin mijin da zaki burin aure ne, sai dai gskya ina tsoran ldan yasan koke wacece ban tunanin zai aureki.
Bariki dan shuru tayi can tace, toh ai nima ba aure
nace ina so ba, bariki na fito,.
Habib yace oh ni habiba rabo na kiran mutum yana
gudu, wlh zaki ci dukiya iya dukiya ga sarauta, ga guy din ya had’u, amma naga akwai miskilanci.
Bariki tabe baki tayi, tace habib kasan n ……..
Dakata Mlm habib ya Katseta, wlh zan miki bura uba, wai mai yasa kike min haka yar A dince kike kyashin karasawa, gaskiya banso yana maganan yana wani daure fuska tare da hararan bariki shi’a dole ranshi ya baci.
Bariki tace yakuri kawata Tabe baki yayi tare da fad’in hakuri kaya ne.
Bariki tace kawata babu abunda na tsana kaman in yaudari mutanan kirki, kince wannan badan hannu
bane, aurena yake son yi? Habib yace kwarai dagaske. Bariki tace bazan iya soyayya dashi ba, yafi karfina.
Habib ya tabe baki, tare da fad’in kaman ya yafi karfin ki? Haba bariki ai babu namijin da yafi karfin ki, kalli madubi ki gani mana kina da kyau na
bugawa ajarida.
Bariki tace hakane, niba mutuniyar kirki bace, bazan yaudari mutanan kirki ba, hawaye ne ya zubo mata a ido, da sauri ta goge dan Kar habib ya gani, but is too late dan ya riga da ya gani.
Yace Mai zan gani haka? Bariki Kece kike hawaye? Babban magana, toh amma miye dalilin ki na cewa ba zaki yaudari mutanan kirki ba, aiba ke kika ce
kina sonshi ba.
Bariki tace kawata mutanan kirki suna da kyakyawan zuciya, suna saurin yarda da Abu, in zaki fadi gskya kawata keda kanki kin San
mutumin kirki kamili bai dace dani ba. Habib yace a’ah Wlh.
Bariki tace nidai yanzu bazan ganshi ba dan ban
shirya aure ba.
Habib yace ban son bariki Mlm, Kar kisa ya maidani karamar mace, mai magana biyu, dan kawai nace miki kamili ne, Aiba daka nan yake ba, ki bari ki had’u dashi sai ki gane ko Waye shi.
Bariki shuru tayi tana nazari, can tace hakane zan had’u dashi, ka bashi number dina zan gane koshi Waye.
Habib yace yanzu naji Batu. Bariki tace yau wani mai kid’a ne zaiyi wasa? Yace masu kid’an kwarya yau muka gayyato.
Bariki tace Kai yau zamu ra’kashe.
*************
Yarima ya koma Gida, koda ya isa gefenshi ya shiga domin yayi matukar gajiya, yana shiga bedroom dinshi kwanciya yayi akan gadon d’akin tare da lumshe ido, yau yana cikin farin ciki domin nan bada dad’ewa ba zaiga yarinyar da yake burin gani
wajan shekara da shekaru.
Ya dad’e yana kwance yana tunanin bariki, son yarinyaryana kara shiganshi koda yaushe, d’auko drawing dinshi yayi yana ta kallon fuskanta yanda take murmushi saiya kara mata kyau,jin karan wayanshi yasa ya ajiye hotan tare da d’aukan wayan, limam ya gani da sauri ya danna tare da d’auka, ban San mai limam yace mishi ba naji yace OK gani nan zuwa, tashi yayi tare da shiga toilet yayi wanka Jim kad’an sai gashi ya fito, shiryawa
yayi cikin wata shadda Mai ruwan sky blue ba karamin kyau yayi yasa hula ya fita domin gidan sarauta Indai zaka wajan Mai martaba ko Yarima
dondole sai mutum yasa hula, fita yayi dan zuwa wajan limam.
Koda Yarima ya karasa suka gaisa da limam cikin
girmamawa.
Limam gyaran murya yayi tare da fad’in Nakira ka kaman yanda nace zan nemeka.
Yarima yace hakane Allah gafarta Malam.
Limam yace akan maganan da mukayi dakai kwanaki akan yarinyar daka fad’amin, Nayi istahara naga akwai alherai da dama a tare da ita, sai dai abunda ban gane ba shine akwai wani boyayyan abu a tare da ita wanda in ba’ai wasa ba zai iya hana ka samunta, inaso ka dage da addu’a akan zabi mafi alkhairi.
Yarima shuru yayi yana nazari, can yace nagode Mlm tare da tashi yabar wajan.
Direct gefen mum dinshi ya nufa inda ya sami Mai martaba yana nan, zama yayi sannan ya gaida iyayen nashi,
mai martaba yace ya hanya? Yace lafiya kalau Abba
Mum tace ansha hanya ya sirikar tawa?
Kai ya dan Sosa cikinjin kunya yace tana lafiya. Tambayan mum yayi tare da fad’in ina Hafsat? Mum tace Tana dakinta.
Tashi yayi ya fita, d‘akin lil sis din nashi ya shiga inda ya ganta tana karanta wani novel, fisgewa yayi da sauri ta d’ago ganin dan uwan nata yasa ta saki kara tare dayin hugging dinshi
Tace saukan yaushe?
Yace ban dad’e da dawowa ba, inata magana kinyi shuru kinyi nisa wajan karanta littarl. Tace bros Littafln ne akwai dad’i.
Murmushi yayi tare da zama inda suka fara fira cikin so da kauna.
Hafsat tace ya sister dina hope Tana lafia?
Jan Hancin Hafsat yayi tare da fad‘in kije katsina saiki tambaye ta.
Dariya Hafsat tayi Sosai sannan tace bros sai dai muje tare kafata kafar ka.
Tashi yayi tare da fad’in inna zauna dake saiki samin ciwon kai bye.
Dariya tayi shiko fita yayi ya nufi gefenshi koda ya shiga sintiri ya dingayi a d‘aki yana tuna abunda liman yace, toh miye boyayyan abun? Ya kamata in sani, tunawa yayi da gidan da yaga habib yace k0 bai tambaya ba yasan gidan karuwai ne, Toh miye dangartakar yarinyar da wannan dan daudu din? Kai something is fishy I have to find out. Wata zuciyar tace karka manta ance gidan y’an uwanta tazo Kar kayi Mata mummunan zato, ka had’u da yarinyar farko Kaga yana yinta Kafin ka zurfafa tunani, wannan tunanin da yayi shine yasa yaji duk wani tantama da yakeyi ya kawar, yace bana tunanin zaki Aikata hakan domin Fuskanki ta mutanan kirki ce.
. Bariki ce cikin wani crazyjeans da wata Shegiyartop Wanda saman ya kama kasan kuma ya bude, gaba d’aya duk wata sura dakejikinta kayan Ya bayyana su, tayi mugun kyau duk da batai makeup ba, kanta ko d’ankwali babu, fita tayi zuwa wajan da ake kid’a karuwan gidan suna ta rawa, ita kam tsayawa tayi tana kallo, habib ne yazo inda take tare da fad‘in bariki ya naga baki shiga cikin rawan ba?
Bariki tace kid‘an ne bai tsuma ni ba. Suna tsaye suka hango khairat itada mutumin da suka gama fadajiya sukai majuna zagin kare dangi sai gasu yanzu suna tare suna ta dariya.
Habibyace oh in kana bariki zaka ga Abu iri iri Kinga y’an iska jiya Sun gama kwasan y’an kallo yau kuma gasu can suna soyewa oh ni habiba.
Bariki tace toh yana zuwa ana bashi gindi yana ci ai dole ya manne Mata.
Habibyace ah naga alama hala ta wanke mai ne yasha wannan rashin mutunci da suka tsundumajiya amma har ya dawo yau, yana maganan ne yana kama kugu.
Ya kalli bariki yace na turama yarima number dinki dazu, Nasan koda yaushe zai iya kiranki inya kira saiki nuna mishi keta Allah ce, mi’ka mata card din yarima yayi yace ga Katin shi numbers dinshi suna ciki duka, dan karya kiraki ki d‘auka ki kwafsa, amsan card din tayi Mai kyau taga an rubuta yarima Aliyu ga tambarin sarauta ansa a card din ga numbers dinshi guda uku da emai| dinshi a jiki, murmushi ta saki tare da tsintar kama da son ganin wannan Yarima din, taga Ya yake domin yanda habib yake kozan tashi abun yayi yawa, suna
nan tsaye saiga ij babba shida Haulat Sunzo. ij babba yace wace wainar kuke toyawa
ne? Haulat tace tambayesu dai, ni naga kwana biyu suna makale ita da habiba,
ij babba ya tabe baki tare da kallon habib yace wani dadiron kika had’a mata da taji dadinsa yasa ta manne miki ?
Habib yace ah yau naga idi zindir, wannan tambaya sai kace ina zaune gidan Radio ana
interview dani, gaskiya bana so ance damai dami tayi sata. Haulat tace in tayi wari maji ai. Habib yace Toh Uwar kini bibi aiko fasa gurbi yayi bakiji. Ba
Bariki tace kanku akeji shiga filin rawa tayi ta Fara kad’a duwawu Tana juyashi ganin haka yasa Haulat itama ta shiga nan Suka fara li’ka ma masu kid’an kud’i Anata ma bariki kirari, bariki na rawa ij babba yazo yaja hannunta tare da fad’In tawo akwai magana, bayan sunje wajan da babu hayaniya ya kalleta tare da fad’in alh madu yanzu Ya kirani yace in fad’a miki ki d’auki wayarsa yana son magana dake.
Bariki tace in dauka inyi mishi Uwar me? Wlh ij babba kibar wannan dan iskan mutumin babu ni babu shi kuma Wlh saina rama abunda yayi min, shi ayabarsa karama ba dadinta nakejiba, gashi babu y’an wasanni balle in rage zafi sai dai kawai ya saka maka ayaba cikin gindi yanda kasan ana Wasan yara, ni Wlh babu abunda zai kara had’ani dashi tsohon
banza yana gaf da rami amma yana binjikokin sa, matsiyaci,
Hajj babba yace ah Abun haryakai haka? Toh fah Tashin hankali, nidai ki dubi mutunci na kiyi hakuri Wlh mutumin nan sonki yake duk yabi ya damu.
Bariki tace yana dai son kayan dad‘i
Hhj babba shewa ya saki tare da fad’in kaji tsohon banza haryasan dad’i, au Ashe sulhu nake, nidai bariki kiyi hakuri yace ran Friday zai shigo kaduna kuma danke zai zo, ki daure
ki d‘auki wayarsa.
Bariki tace shikenan zan d’auka tunda kince amma fah saina rama abunda yamin dan sai
na nuna mishi niba Kalan karuwan da ake duka bane inyi shuru.
ij babba yace oh waike bariki Abu bai wuce wane a Wajanki ,ki duba fah kiga wannan mutumin da girmansa yake lallabaki aiko darajan girman nashi kya hakura.
Tace wani girma? Ai tunda ya tube tsirara a gabana naga komai kallonshi nake kaman Sa’a na, ni a wajena bashi da girma dan ya zubar dashi.
ij babba yasa hannu a baki tare da fad‘in ah yau Ina ganin sabon salo, nima kam bari in
fara rufe nawajikin Kafin ki gane min komai.
Dariya bariki tayi tare da fad’in hjyta Aini dake duk abu d’aya garemu inna gani ma ai babu
damuwa. ij babba yayi gaba yana botsare duwawu tare da fad’in karki lalata ni.
Tana tsaye ‘tana dariya taga ansa Mata wani abu a hanci tun daka lokacin bata san inda
kanta yake ba.
Koda ta farka ta ganta cikin wani d’aki Mai datti duk yayi kura waige waige ta farayi tare da fad’in inane nan? Jin karan kaman za‘a bude kofaryasa ta tashi mai kid’an nan taga ya
shigo, tace dama kaine ka kawo ni nan?
yace kwarai kuwa, dama na fada miki, Kinga nan babu kowa, zanyi abunda nake so inyi dake kuma Bari kiji bazanyi amfani dake da condom ba saboda ina son in saka miki cutar
dakejikina wato HIV.
Bariki tace karka fara yin wannan kuskuren, kai baka isa ka taba koda yatsa na bane balle gindina.
Dariya yayi tare da fad’in bari in nuna miki, matsowa kusa da ita yayi tare da cafko ta, yace gashi na taba ki, tureshi ta farayi amma ina taga ya Mata ri’kon gaske, kokarin cire mata riganta yake yana fad‘in ai koda mutuwa za kiyi yau sai naji irin naki zumar Wlh tunda na ganki na mutu da sha’awarki, cire mata rigan yayi daga ita sai brezia dajeans din dake jikinta yace Kai kalli nono masu kyau yau zansha dad’i bariki tace kana aikata kuskure wani Wawan Mari ya sakar mata Wanda saida taga stars yace kuskuren uwarki ai Wlh yau saina ciki tunda na kawo ki nan gwara ma ki bani hadin kai tun Kafun in illataki ……
Hmmmm ana zuba bariki anan