MIJIN DARE CHAPTER 3 BY R.HUSSAIN
MIJIN DARE CHAPTER 3 BY R.HUSSAIN
_____________Waye ne, Khaleesat ta faɗa ta na tsaye bakin ƙofar gidan nata, Ibrahim Mijinta ya amsa “ni ne dear ”
Buɗewa ta yi ganinsa a ƙasa ba tare da motarsa ba ta bi shi da kallo, “lafiya ka dawo?”
Murmushi ya sakar mata yana shiga ciki, ya ce” mantuwa nayi na decument ɗin Company da na shigo da su jiya da daddare, bin ta yake da kallon sha’awa,ya wuce bedroom ya ɗauko ya na zama bakin gado haɗi da zuba tagumi hannu biyu, shigowa ta yi ta na cika ta na batsewa, “ka ɗauka, to ka koma mana”
Ɗagowa ya yi ya kalleta yace ” yau ni kike kora dear, wai me yake damun kanki ne”
Khaleesat tace” ni ba korarka na yi ba, ka yi ta zama kar Allah ya sa ka koma” ta fice a ɗakin. Kitchen ta nufa dan ɗora girki kafin Yaronta ya dawo, tuno mafarkin da tayi ɗazu ya sa ta ajiye komai ta koma ɗaki domin yin wanka, ya na zaune inda ta bar shi, kayanta ta cire ta nufi toilet, jikin Ibrahim na rawa kuwa ya bita, ko Allah zai sa ya dace.
Tana wankan ta ganshi ciki, “me ye hakan ka ke yi ne, dan Allah ka fita anan”
Cikin dakewa irin ta barazana yace” ba inda zani sai kin ba ni haƙƙi na yau Khaleesat”
Cikin tashin hankali wanda batasan dalilin yinsa ba ta janyo towel ta na ɗaurawa ta fara masifa”to dole ne na ce ba na so, ba na so ko,ka ji jaraba” nufar ta ya ke ta na ja baya, “wallahi yau ko za ki mutu sai nayi”
Kokawa su ka fara tun daga toilet ɗin ya samu nasarar cire towel ɗin, ɗaukota ya yi cak, ya ɗora ta a gado, miƙewa ta ke ƙoƙarin yi,ya gwada mata ƙarfi danneta ya yi, ya fara samawa kansa satisfying da ita, gajiya ta yi da shure-shuren ta ƙyale shi, amma sai zaginsa ta ke yi, ko ajikinsa aikinsa kawai ya ke yi, sai da ya ji ya fitar da duk wani abu da yake damunsa a cikinsa,sannan ya barta kwance ta na ta kuka da Allah ya isa.
Ko kallonta baiyi ba ya miƙe yace”Allah ya yi miki albarka, ya shirya min ke” ya nufi bayi, tsaftace jikinsa ya yi sai farinciki ya ke, ya fito ya ganta ta na nan kwance ta na kukanta, yace” to wai kukan na me ne ne, Ummu Ansar, kuma aunty’n Humaira naga abun nan ba wai ni kaɗai na ji daɗin ba ko”
Hayayyaƙo masa ta yi, to cewa nayi dole sai kayi, iye mutum sai jarabar tsiya” bai ƙara tankawa ba, ya ci gaba da shirinsa, wayarsa ce ta yi ringing ganin Oga M.D ne ya sa ya amsa ” na ɗauko,ina hanya”
Daga can aka yi magana yace “okay,okay sorry sir” sannan ya kashe wayar.
“Yanzu haka zan koma babu abinda za ki ba ni naci” Ibrahim ya faɗa ya na ɓalle lence ɗin hannun rigar kayan da ya sauya.
Da masifa tace” me zan baka banda wanda ka ci yanzu mtswww ta ja uban tsaki, sai harararsa ta ke yi” dariya ya sa ya na ɗaga mata hannu ” see you sweetie” ya fice ya koma Office ya na jinsa fresh.
Duk abin nan da ya ke faruwa MIJIN DARE na gani, ya samu nasara akan Khaleesat amma ya kasa samon galaba akan Ibrahim, duk yanda ya so ya ji ya tsani Matar tasa, su dinga faɗa tsakaninsu abun ya gagara.
Sa bo da Ibrahim mutum ne mai tsananin ibada, baya wasa da addu’a.
Sai da ta gama tsine masa, sannan ta je tayi wanka ta ɗauro alwala tayi sallar azahar, jin yanayinta ya sauya tasan Ansar ya tashi, ta na shirin tashi taji Humaira ta na bugu, zuwa ta yi ta buɗe ƙofar, idanunta jajir alamar ta ci kuka, Humaira tace” aunty me ne ne ya sami idonki?”
Yaƙe tayi tace” bacci nayi ne sai kuma na yi wanka, shine na sa sabulu ban kula ba, ya tashi ko?”
Humaira tace”sannu” ta na kwance goyon Ansar ta bawa Mamansa.
Ki shigo mana” Khaleesat ta faɗa, kai Humaira ta girgiza alamar a’a tace” lokacin islamiyya ya kusa zanje in shirya ne”
okay ina zuwa, komawa Khaleesat tayi ta ɗauko mata allbutter biscuits guda biyu tace “ga shi nagode”Humaira ta karɓa tayi mata godiya ta tafi. Kulle ƙofar ta yi, ta zauna a parlour ta na bawa Ansar nono, idan ta tuno Ubansa sai ta gallawa jaririn harara, ƙarshe ma cire masa nonon tayi ta ce”ba za ka sha ba, Ubanka ya ja maka” Yaron da ya ke mai haƙuri ne haka ya yi shiru ya na ta kalle-kalkensa.
Zaune su ke a babban Office ɗin Ma’aikatar Ibrahim ya shigo ya na ba da haƙuri akan rashin isowarsa da wuri.Taron ƙara faɗaɗa harkar zane-zanen da ɗan Alhaji Alhassan Nuhu zai buɗe wato SHANSUDEEN ALHASSAN NUHU, wanda ya ke garin Lagos, cikin ikeja, shi ne a ka ware amintattu daga cikin ma’aikatan company’n ana meeting akan sabuwar ma’aikatar da aka buɗe wa Shams na zane-zane za’a ɗauki sabbin ma’aikata Architects a ciki, sai da aka gama tsab, sannan Ibrahim ya nemi alfarmar a bar shi zai kawo Messanger idan ba damuwa,amincewa aka yi,aka tashi daga meeting ɗin.
Babu wanda ya zo ran Ibrahim sai Malam Ayuba mai kayan miya, kullum idan zai wuce sai yaga kayan miya na baya, ko ba zai sai komai ba sai ya tsaya ya ce a ba shi wani abun na ɗari biyu ko uku, sai ya miƙa masa dubu ya ce ya bar canjin, tausayinsa ya ke ji shiyasa ya nema masa aikin Messenger a sabon company da ake shirin lunching ɗinsa.
Malam Ayuba mutum ne mai son kansa,ba ya wadata iyalinsa hakan yasa ba ya samun wani abu a kasuwancin nasa, ga ƴarsa Inteesar da ya kasa haƙuri da jarabawar da Allah ya yi masa a kanta,kullum kyara da tsangwama ne tsakaninsa da Yarinyar, da akwai bolar da zai kaita da tuni ya kaita bolar da ake zubar da Matan da su ka yi jinkirin aure.
Inteesar da ba ta san dalilin hakan ba, idan Uban ya na hantararta sai ta zari gyale ta fice yawon ina da biki ko suna a cashe, idan ta na cikin fushi, ko ɓacin rai to rawa ko bacci MIJIN DARE ya zo ya yi amfani da ita, shikenan wannan fushin zai tafi.
Ga shi ta tsani ƙannenta hantara da kyara ce tsakaninsu.
Wuni tayi yau da ciwon ƙafa, Irfan da yake ɗakinsa ya na haɗa haddar suratul a’araf,sosai ya ke karatun cikin ɗaga murya. Inteesar da take ɗaki tayi tsaki ya fi sau ɗari, a fusace ta nufi ɗakin Irfan tace masa”kai dalla ka cika mana kunne sai ka ce a makaranta ka ke,ka yi iya kanka za ka jiyar, ba cewa mu ka yi ka damemu ba” ya saba da hakan da take masa, ya sa alama a cikin ƙur’anin yace” Aunty kinga ban shiga harkar ki ba,kar ki shiga tawa, kuma na sha gayamiki, ban iya karatu a zuciya ba,idan ba za ki saurara ba,ki fita mana mtsww”
“kutumar Ubanka” ta dan na masa ashar, abunka ga matashi mai tashen bagala ya miƙe tsaye yace”kar ki ƙara zagi na, kinga Umma ta mana tsakan….Kafin ya gama magana ta kama shi da kokawa, abun ka da zuciyar Maza, ya kai mata naushi a ƙirji, ihu ta sa ta hau kuka, Umma da ta ke baccin azahar zuwa la’asar ta tashi a furgice ta fito da sauri.
“wayyo Allah ya taɓa min nonona” kuka take sosai ta na nononta ya taɓa, jin sharrin da ta yi masa ya sa ya fara rantsuwa da cewar ƙarya ta ke masa, wanke shi da mari Umma tayi, “abun da ka koya kenan Irfan, munafuki zo ka fice min a gida, lalataccen banza,zo ka fita nace” baƙin cikin abinda Inteesar ta yi masa ya sa Irfan kuka, ɗaukan ƙur’aninsa ya yi ya fice daga gidan.
Ke kuma ballagazar banza, ki na yawo tiɓi-tiɓi a tsakar gida haka, ba dole su dinga taɓa ki ba, za ki tafi ko sai na mangare ki” Inna ta faɗa da tsawa. Inteesar ta koma ɗakinta ranta fes, ta hana karatun da yake, an ma kora shi waje.
Ta na shiga ɗaki ta kwashe da dariya ta na faɗawa kan ƴar katifarta, abinda ba ta sani ba,akan Aljanin da ya kwanta ya yi ɗai-ɗai ta faɗa,babu ambaton Allah ba komai.
“Ni zai takurawa dan Uwarsa na fisa hauka ai, gobe ma ya ƙara, wash ƙafata” ta fara mammatsa ƙafar dan ciwo take mata sosai Aljanin da shi ya sakar mata ciwon ƙafar ya na kallonta ya na ta dariya, aboniki ta ɗauko ta shafa, jin zafi ta ke a jikinta hakan yasa ta cire best ɗin da ke jikinta wacce ko bra babu, ta ja zani sama ta na ta fama da ciwon ƙafa, zingurinta Aljanin ya yi ya saukar mata da kasala jin amfara kiran sallar la’asar, bacci mai nauyi ne ya kwasheta, bushewa da dariya Aljanin ya yi sannan ya ɓace.
Imran ne ya shigo da kekensa, sallama ya yi yaji gidan shiru, ga shi la’asar ta yi, ɗakin Umma ya leƙa yaga bacci take yi, tashin ta yayi yace” an shiga sallah” buta ya ɗauka ya yi alwala ya tafi masallaci, Umma ma ta fito da hanzari dan yin sallah, ganin ɗakin Inteesar a rufe, ya sa tayi zaton ta fita ne, dan ba wai sanarwa take ba idan za ta fice, musamman in Umma na bacci, ko da anyi mata faɗa ba ji take ba, gobe ma sai ta yi.
Mafarki take yi,ana taro a wani baƙin daji, ga wasu halittu nan masu ban tsoro suna ta cashewa, ita kuma ta na zaune tare da wani mutum ana suna ta haihu,sosai suke murna ba tare da tsoron wannan halittun ba, ji tayi halittar da ke kusa da ita yace”Matata, yau kin haifa min ɗa na huɗu kenan, kinsan cewa ba ki da Miji sai ni ko, duk abinda kike so ki gaya min zan mallaka miki shi kafin ƙiftawar idanunki, ce masa tayi Irfan ya na damuna da karatu ba na so, idan ya na yi sai inji kamar raina zai fita” ɓata rai MIJIN DAREn ya yi yace” ba zan iya yi masa komai ba, idan na matsa masa zai iya hallakani, bar ganinsa ƙanin ki ne, Yaron ya na da dafa’i ba ya zama ba alwala, ya na azkar safe da yamma ba ni ba, duk wani abu na cutarwa ba zai iya cutar da shi ba, wannan aikin da kanki za ki yi kinji Matata” rungumota ya yi yana sakar mata kiss da wawakeken bakinsa mara kyan fasali, a razane ta farka “mtswww wai ni na haihu ko yaushe nayi auren ma, da zan haihu aikin banza” miƙa ta yi ta ɗauki brush ta fita wanka tayi ta fito alwala tayi ganin Umma na tsakar gidan ta koma ɗakin ” wallahi ba sallar da zanyi yanzu sai anjima” shiryawa tayi sama da minti 30 tana kwalliya (Sallar da ba za ta haura minti biyar zuwa goma ba, ta gagara, Ya ubangiji ka kiyaye mu daga sharrin shaiɗanu, mutum da aljan,Ameen).
ƴan kayanta da ba su fi kala goma sha biyar ba, ta duba ta ɗauko wani material ta ɗauko bra da pant ta saka ta zura material ɗin, jin ƙaiƙayi tayi a nipple ɗinta ta duba gani tayi har tsatsafo da ruwa yake tamkar wacce take shayarwa, mamaki tayi kawai ta share ta ci gaba da shirinta, ba ta da wasu hijabai sai guda biyu koɗaɗɗu da sakawa za ta yi, ta fice dan ƙafarta har ƙaiƙayi take ta fita waje,ajiye wa tayi ta ɗauki mayafinta mai kama da abun tatar koko ta sa,tace”Umma bari in leƙa gidansu Hafsa”
Umma tace”to ni me zance miki Inteesar ko na hanaki ba hanuwa za ki yi ba ai”
“kai Umma ke kullum cikin faɗa haba dan Allah, zama zan tayi a gida kuna min gorin rashin Mijin aure, kamar ni zan kawowa kaina mtsww” ta yi ficewarta.
Gidan su Hafsat ta nufa, ta na shiga ta……….
DOMIN KARANTA CI GABA DUBA 👇