MISBAH BOOK 3 CHAPTER 12 BY SA’ADATU WAZIRI GOBE

MISBAH BOOK 3 CHAPTER 12 BY SA’ADATU WAZIRI GOBE

 

 

Dama nina rabashi da wannan abin da yake

Alla ya ya ba ni damar maida masa, sai dai kafin in

kai ga daukar wani hukunci ko zuwa Lagos din, sai

na yi magana da shi, na ji ta bakinsa, in ya so sai

mu je ni da ke mu samu Bahijja mu yi mata

magana ta hanyar nasiha da fahimta, ba ta nuna jin

zafi ba ko tsangwama ko nuna mata Farida tamu ce ita ba tamu ba.

“Saboda ni

na yarda

da yarinyar nan da

tunaninta da al’amuranta, ba mace ce mai son

zuciya ba, sai dai kawai kishi irin na mata, dan

haka ina ganin mutuncinta da girmanta kuma ina jinta kamar diyata, dan haka mu bi abin nan a hankali mu fahimtar da ita, ina fata kin fahimce ni

Hajiya Aisha ta girgiza kai na fahimta,

“ba zan

ki ta taka ba, sai dai kam insha Allah auren Farida da Deeni ba fashi.”

Ya kalle ta ya girgiza kai ya ce,

“Dadina da mata

saurin mantuwa da gajeren tunani,”

“miko min

wayata in kira Deeni.

Bata bata lokaciba ta mika masa ya kira shì a

bugu na hudu Deeni ya amsa tare da yin Sallama, yanayim muryansa ya san cewa eh lallai yana cikin

damuwa, bayan sun gaisa ya ce,

“Deeni lafiya ko?”

Ya dan gyara murya ya ce,

“lafiya Baba, ya su

mama?”

“Lafiyanta kalan, da ma munz0 da wata shawara

ce ni da mahaifiyarka, amma fa in ka yarda ka

amince ba lallai ba tilas Deeni, ni ko ina ga mai zai hana ka auri Farida, matar danuwanka da ya rasu

wannan ka ga ka rufa wa iyalansa asiri, haka nan

yaransa ba za su yi maraicin rashin uba ba kuma ba

za su rabu da uwarsu ba, ba za kuma su je agola

gidan uban wani ba tunda Allah ya ba ka ikon da wadata kuma wani abu ne da ton farko ka so Allah bai kaddara ka samu ba, sai yanzu kaga kuma za

ka samu lada har a gun Allah.

Ras! Deeni ya ji gabansa ya fadi, wani tashin

hankalin iyayensa ke son sake jefa shi, da ma

Misbah na zarginsa sannan ga tashin hankali da

rashin fahimtar dake tsakaninsu sannan shi har cikin ransa ga Allah ba ya son Farida, ba ya son

Aurenta, rayuwar auren da ya shirya suka shinfida

shi da matarsa ya fi masa komai jin dadi irin hakuri

da fahimta da Misbala ke masa, irin na yanayin

tsarin rayuwarsa da aikinsa, ba ko wacce mace za

ta iya masa wannan fahimtar da UZURIn ba, sam

shi ba ya son wani rikici ko rudani a rayuwarsa.

Allah ya ce in za ka yi adalci ka kara aure, maganar

gaskiya ba zai iya adalci tsakanin kowacce mace da

Misba ba, koda kuwa Farida ce.

Alhaji ya katse shi

‘Deeni, kana ji na? ya na ji

ka yi shiru?”

ina ji Baba, gaskiya ba dan za ku ce

na muku rashin biyayya ba gaskiya ni dai ba ni da ra’ ayin ko sha’awar kara aure,

su Deeni kuwa

yarana ne duk abin da zan iya yi wa dana ko uba zai yi wa da suma haka zan musu, zan iya dawo

da su gidana in mamansu za ta amince isakanina da

Farida abu ne da ya wuce.

“Zaman lafiya

da kwanciyar hankalin dake

tsakanina da Bahijja ya fi min komai, ba na son

wani rudani ko tashin hankali

a rayuwata.”

Mahaifin ya katse shi da cewa

“Deeni kamar baka

fahimce ni ba, yara ne ba na so a raba su da

uwarsu kuma karsu je gidan wani agola

sadaukarwa ce nake so kayi kuma Farida wata abu ce da ka so kuma kake so.

Baba me ya sa kake son ruda abubuwa ne? ka

na hada da da yanzu, Baba har yaushe za kuna min haka? lokacin da nake son Farida kun hana ni yanzu kuma da na manta da ita na ci gaba da

rayuwata kuna son dawo da ita lokacin da ba na bukata, Baba kubar ni in samu kwanciyar hankali,

da can kun jefa rayawata cikin rudani da kunci,

yanzu ma kuma son sake haka, ba na da bukatar

kara aure ko wata mace a rayuwata in ba Bahijja

ba, don Allah ni ba yaro ba ne yanzu, na san me nake, na san

ciwon kaina, ba na bukatar kuna

yanke min hukunci a kan rayuwata, Baba alkawari kamin tun kwanaki ba za ka sake min shisshigi a rayuwata ba to, ban san me ya sa kake son canza

maganarka ba.

“Don Allah Baba ka bar maganar nan, ku yafe

min, ba zan iya yin abin da kuke so ba.

Bai saurari

me mahaifin na sa zai ce ba ya ajiye wayar, tuni ran Hajiya Aisha ya baci ta dinga ji zuciyarta na

mata, kuna da zafi domin kuwa ta ji duk abin da suke fadi saboda a speaker ya sa wayar wato da gaske ne Bahijja ta mallake mata da tana zaune ba

ta sani ba, ta yadda ta san Deeni na son Farida, wani

abu ne mai wuya a ce soyayyar nan ya tafi har yana

kin aurenta gaskiyar Farida ne, saboda Bahijja ne yake gudun auren Farida, amma ba ta isa ta hana

yaranta da jikokinta abin da suke so ba, tsintacciyar

mage mara asali ta samu wuri, shine za ta hama

wani shiga.

“Farida da Deeni tare da jikokinta za su zauna a inuwa daya inuwar aure gida daya, ni zan je Lagos

din da kaina in samu Bahijja,

ta fada cikin bacin rai tana kallon Alhaji ya ce,

“za mu je tare, amma

mu bi abin a hankalì ba tashin hankali a ciki.

“Na sani Alhaji, zan je in kalli fuskar Bahijja, in

tambayar wa Deeni izinin auren Farida tunda shi ba

zai iya ba, zan ga yadda za ta ki amincewa da

batuna.

Deeni kuwa ransa ya mummmunina baci da

maganar mahaifinsa, yanzu ma yana cikin wani

tashin hankali, meyasa iyayensa kullum suke masa

hakan? Wannan karan ba zai iya musu abin da suke

so ba, ya tuno kwanansa uka ke nan rabonsa da

gida yana ga lokaci ya yi da zai koma su daidaita

da Bahijja, ya kawar da duk wani rashin fahimta

dake tsakaninu saboda ya san dai yanzu kan ta

huce, za su yi magana ta natsuwa da fahimta.

Sun iso Lagos bayan Azahar, gidan suka

wuce kai tsaye, sai dai ba su samu kowa

ba, kasancewar ba su sanar da kowa suma

zuwa ba, su Baba Audi sun masu hidima sosai

kasancewar sun san muhimmancinsu ta ce zata buga wa Bahijja waya, Hajiya Aisha ta ce ta bari

kawai, in sun yi sallah za su je office din su same ta, haka ko aka yi ba su bata lokaci ba suka fita,

abincin da aka kawo masu ma sama-sama suka ci,

suna fita suna

Allah-Allah su je wurin Bahijja

domin sunyi abin da yakawo su.

Sun same ta a office dinta zaune tana duba

report din was marasa lafiya, suka yi sallama da ta

gansu ta mike da sauri ta tare su cikin girmamawa ta musamman

tare da nuna mamakin ganinsu

“Hajiya, kuma haka ba labari ai da na bar zuwa aikin ma da na san da zuwanku.

Hajiya Aisha ta dan yi murmushi,

“ai ba komai

ga shi mum zo gara dai da kika zo ai kinga kin rage aiki.

.»* A take Bahijja ta sa aka kawo musu abinci da abin sha na alfarma. Bayan sun ci sum sha, ta ce, za mu wuce gida saboda ku huta?”

“Ah’a” in ji Alhaji,

“in kin ga mun bar nan to,

mun yi maganar da ta kawo mu,Babijja ta kalle

shi ta ce,

“Baba ai da ba sai kun zo ba, da sai mu

mu je har inda kuke,

Hajiya Aisha ta karba ta ce,

“Ai tunda kika ga munzo to, maganar tana da

muhimmanci ne, gaban Bahijja ya tsinke,

“ba dai Deeni karata ya kai gida ba,

ta fada a zuciyarta

HMmm LABARI fa nata Tafiya shin KOYA ZATACI GABA da KAYAWA KUDAI KUCI GABA da kasancewa damu A koda Yaushe

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button

You cannot copy content of this page

Adblock Detected

YOU ARE USING ADBLOCK TURN IT OFF TO COUNTIUE BROWSING OUR WEBSITE