MISBAH BOOK 3 CHAPTER 15 BY SA’ADATU WAZIRI GOBE

MISBAH BOOK 3 CHAPTER 15 BY SA’ADATU WAZIRI GOBE

 

Hajiya ta fadà tana kallonta tana dariya ta ce,

“na gode Bahijja da hadin kai da kuma fahimtar da kika mana komai yazo cikin sauki son da kikewa Deeni

da kuma girman da kika ba mu matsayin iyaye kin cikawa Deeni burinsa na auren abin da yake so yake muradi, da Deeni da Farida basu da burin daya wuce na su mallki juna, mukuma iyaye ba mu da burin da ya wuce burin yayanmu wannan

sadaukarwa da kikayi Allah ya baki ladansa ya rufa maki asiri duniya da lahira.Ta yi murmushi tare da fadin “Ameen. tausayin

kanta taji ya kamata ta tsinci kanta cikin wani irin kewa da raunin zuciya duk karfin hali irin nata sai

da taji kuka mai karfin gasket yazo mata abin da ta tsana ke nan tsintar kanta cikin wannan yanayin

duk da ta san ita marainiya ce karo na biyu ta sake tsintar kanta cikin maraici ta so kai su Airport

amma ta gagara da kyar ta iya tsaida kanta tayi

musu sallama tare da musu shatara na ariki kamar yadda ta saba ta rakasu har mota sannan ta dawo

ciki ta nufi dakim Baba Andi ta sameta zaune kan sallaya tayi jigum dan kuwa itama tasan meke

faruwa Deeni ya fada mata ko za tayiwa Bahijja

magana ko za ta saurareta dan tana jin maganarta donta  dauke ta tamkar mahaifiyarta.

Sai dai Baba Audi itama tabi bayan Bahijja

saboda ta naga hukuncin data yanke shine daidai

dan haka tana jin tashin hankalin Bahijja tamkar

nata tashin hankalin, Bahijja ta fada kan cinyar

Baba Audi ta fashe da kuka mai karfin gasket Baba Audi bata tsaida ita ba  yana da kyau tayi kukan ta samu saukin

abin da takeji a zuciyrta. sai da tayi kuka mai isarta

sannanta mike ta kalli Baba Audi ta ce,

“Baba Audi

na gode da kika bani wanna damar har na samu cinyar da zan kwanta inyi kuka na samu wacce ta

tayani jin zafin da nuna damuwa dani da halin da nake

ciki?* Baba Audi ta share hawayenta ta ce,

“in ban damu

da ke ba Bahijja dawa zan damu? Kina marainiya baki da kowa, ni da nake bani da da ba jika sai dangi wanda suka jima da ya dani saboda na zame

musu kaya gashi bani da komai sun gaji dani da talauci na da yasa ko nemana ba sayi dan haka ni da ke muka zamewa juna

‘yan’uwan juna a

musulunci kin darajani kin mutuntani fiye da tunani na ko yata ba za ta min abin da yafi haka ba.

Bahijja ta share hawayenta tayi murmushin

bacin rai ta ce,

“Baba Audi kin san a rayuwar nan

akan mutum irin kamar mutum

yayi maka alfarma a rayuwa har ya zame maka

nauyi da kaya akanka ka rasa dame zaka biya su zama da wannan nauyin abu ne mai wuya dan haka

yau na samu sauki, kauna soyayyata da iyayen Deeni da

“yan’uwansa suka nuna min yau na

biya su alhamdulillah ina da abin da zan iya biyansu da shi so da Deeni ya nuna min darajar aure da ya bani yau na biyashi da abin da ya fiso a rayuwa da

Deeni ina ganina kullum cikin shaukin Farida da begenta amma saboda ni yaki aurenta, Baba Audi

ba zan iya rayuwa haka ba ina tare da miji amma

Kullum hankalinsa nakan wata ko yana tunanin

wasu daban wannan ba nasara bane a tare dani sai

faduwa wannan ba ci gaba bane ci bayane a tare dani.

Deeni ya auri Farida da duk yan matan da yake

so yake muradi yake buri shine nasara ta ya samu

duk abin da yake so yake bukata abin da iyayensa

da sauran yau uwa ke son masa suke bukata dan haka yau bani da wani sauran nauyi ko fargaba ko

tashin hankali a gabana yau din nan yanzun nan shine rana lokaci na karshe da zan yi kuka in zubar da hawayena akan

Deeni da aurensa ko Wata

rayuwarsa da bata shafeni ba.

Haka nan ba zan sake yin rauni ba akan Deeni

ko wata soyayyata zan fuskanci rayuwata tare da ci gaba da yin abin da zai bani farin ciki da kwanciyar

hankali wanda Deeni baya daya daga cikinsu ni kuma na iya cire duk abin da ke kuntatamin zuciya

da rayuwa a raina soyayyar da za ta sa maka kunci

bacin rai da tsana da jin zafi a zuciyarka da

Rayuwarka ba soyayya bace, baka da abin da zakayi da wanna soyayyar dan haka duk wani

shauki ka watsar da shi ka cireshi a zuciyarka da rayuwarka shine daidai.”

Baba Audi ta katse ta “Bahijja karki yankewa

kanki hukunci cikin zafin zuciya da rashi fahinta”

Ta yi  wani murmushi na takaici ta ce,

“Baba

Audi nasan Deeni na fahimceshi na karance shi fiye da yadda yasan kansa zaman lafiya nake nema wa

kaina wannan kuwa shine zaman lafiyata ba zan kuma biyewa son zuciyata ba, duk yadda tayi dani

sai nafi karfinta da yaddar Allah.”

Tana gama fadi ta mike Baba Audi zan je in

kwanta sai ku shirya mana abinci yau dai kaina na

ciwo ba zan samu leko kicin ba, dan Allah ina so ki

tsaya kisa ido akan abincin Deeni kin san yadda

muke shirya masa komai in ya so sauran kowa ya

da fa abin da ya masa Baba Audi ta amsa mata da

to tare da binta da kallo tana mamakin halayya da

kar fin hali irin nata tana mata addu’a Allah ya

kawo mata sauki a zuciyarta ya kuma daidaita

tsakaninsu.

Deeni dake tsaye a kofa yana jinsu ya din gajin

kalaman Bahijja tamkar tana watsa masa wuta tabbas yasan,,,,,,cikin gidansa

da rayuwar

aurensa me dadi yazo karshe ya rayuwa zata

kasance bai sani ba kin sauke nauyin da ke kanki

kin cire Deeni a zuciyarki shin ni kuma ya zan yida nawa nauyin da ke kaina da ke da ke cikin

zuciyata da rayuwar da kuka zaba min keda

mahaifana yazanyi cikin rashin fahimta?

Deeni na na tsaye yana maganar zuci har Bahija

ta fito ta wuce shi amma tsabar zafin zuciya bata ma lura yana tsaye a wurin bata wuce shi kamshin

jikinta yadawo da shi hayyacinsa ya bita da kallo ta

rikide ta zama wata abu daban tamkar ba Misbah

dinsa da ya sani ba kuma yarasa meyasa ya kasa

kyaleta yana kokarin kawar da rashin fahimta

amma kuma abin sai karuwa yake alamura sunyi nisan da bazasu warware ba.

Dakinta ta nufa tayi alwala tare da daukar

Littafi mai tsarki ta karanta tare da yin addu’a sanna ta

dauko magani tasha bata jima ba kuwa barci mai karfin gaske ya dauke ta har bata san inda take ba

wanna ya bawa Deeni dammar shigowa dakin ya

jima tsaye yana kallonta yana jin tsananin son ta da

kaunarta ga tausayinta a zuciyarsa ga kuma jin

haushinta duka suka hadu masa lokaci guda tare da

tsananin sha’awarta ya lura ta fada ta rame saboda

damuwa nan yaji yana son rungumarta a jikinsa ko

ita ba taji sauki ba shi zai ji saukin abin da ya keji a

ransa yasa hannu ya dauki maganin da tasha

maganin barcine mai karfi wanna ya tabbatar masa

duk taba ta da zai yi ba za taji ba.

Hakan yasa ya matsa dab da ita ya zauna tana

kwance yasa hannu ya dagota ta sauke numfashi

hade da ajiyar zuciya yanajin tsananin shaukinta

na shigarsa hakika bashi da wani shauki ko farin

cikin natsuwa da kwanciyar hankalin daya wuce

wannan me ya faru ne tsaninmu Misbah na? me ya

jawo mana zama cikin wannan yanayi ina sonki

Bahijja ina tsananin bukatarki please karki kyaleni

karki cireni a zuciyarki karki cireni a rayuwarki

zan iya jure komai amma banda nuna min rashim so

Da kike yi, wannan halin ko in kula da ki kike nuna

min yana min ciwo fiye da komai Bahijja ni me

sonki ne ban taba yaudaraki ko maki karya ba.

Hmmm LABARI fa nata Tafiya shin KOYA ZATACI GABA da KAYAWA KUDAI KUCI GABA da kasancewa damu A koda Yaushe

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button

You cannot copy content of this page

Adblock Detected

YOU ARE USING ADBLOCK TURN IT OFF TO COUNTIUE BROWSING OUR WEBSITE