MISBAH BOOK 3 CHAPTER 5

MISBAH BOOK 3 CHAPTER 5

 

 

Shi kuwa Deeni ya tsaya yana kallon su, domin

sun zama abin kallo ya lura Bahijja ta iya biye ma

yara da son hakarsu da biye masu duk tsananin

fada da kishin da take yi da Farida bai sa ta nuna

shi a zahiri ba, mace ce mai iya boye kishinta

musamman a gaban mutane, amma shi ya san

tashin hankalin da yake gaban shi, an yi maganar

Farida ma ya aka kare balle gidan, to wai shin me www.dailynovels.com.ng

ya kawo ta garin Lagos kodai sabon salon son daga

masa hankali da wargatsa masa hankali ne?

Tabbas shi kadai ya san tashin hankalin da za

su shiga shi da Misbah, tana ta iya daga masa kafa

a kan komai amma banda magana a kan Farida,

tana da matukar rauni a wurin. Yana cikin wannan

tunanim sai ga Farida ta katse shi ta ce,

“Sannun ku

da dawowa uncle Deeni,

tana dariya ta ce,

“tun

dazu jira muke amma shiru.”

Bahijja ta ce, “ke ma kamar yaran uncle Deeni,

koda yake haka din yake.

Nan ta yi murmushi ta

ce, ya hanya? da fatan kun iso lafiya, amma

ma’aikatan gidan sun muku kyakkyawar tarba

kamar yadda muka kware wajen tarbar manyan baki na gida.

Ai kuwa Faridan ta amsa “Duk da mu ma din nan

kamar gida yake wurin mu.”

Misbah ta yi murmushi ta ce,

“Yeah, kamar

gida, Hausar ma akwai bambanci, sai dai duk da

haka mu ba mu wasa da baki a gidan nan, mu

karasa ciki in ga irin tarbar da akai maku, ta isa ko

ta yi kadan.

Duk yadda Farida ta so yin maganar

Deeni sai Misbah ta ta ari bakinsa ta amsa.

“Ikon

Allah,

ya ce,

“wannan miskilar in abubuwanta

suka motsa sai Allah.” Tare suka kutsa cikin falon

suka tarar Baba Audi da Baba zulai masu aikin

gida, suka ga an kammala komai, kayan abinci da

na sha kala-kala suka gabatar masu, Misbah ta kalli

Baba Audi ta ce, www.dailynovels.com.ng

“sannun ku, da fatan kun ba su

masauki mai kyau ko?”

Baba Audi ta ce,

“eh, na

kai su can sashen baki na gida amma ta ce,

“dakinki za ta sauka, to, abinki da ‘yan gida ba baki

ba, ban yi mata musu ba.

“A’a, Baba Audi kin kyauta da ba ki yi mata

musu ba, amma mu gidan nan Alhamdu lillah,

Allah ya mana wadata, ba takura kowa ya zo ya

sauka zai sake ya ji dadi,” «ina zuwa, zan je na

shirya wa Deeni bayi yanzu ya yi wanka.

Nan ta

yi ciki, har ya juya zai bi ta sai Farida ta kira shi.

“‘Uncle Deeni ya ko gaisuwa mai kyau ba mu yi

ba balle na fada maka me ya kowa mu

Gaba daya ya rude ya rasa me yake ciki, Bahijja

tana jin su amma ta daure ta yi ciki ta kyale su.

Ya ce,

“ya su mama?”

“Da ma Jamb na zo rubutawa

Ya ce,

“Jamb tun daga Kaduna har Lagos, kin

yanke hukunchin komawa karatun ke nan, amma

tabbas kin yi ma kan ki gata.

Ta ce,

“Eh, dalilin da ya sa na yi register a nan

saboda ya zo da hutun yara kuma suna son zuwa

Lagos hutu, ka ga ni ma in na yi jarrabawa sai na

huta, na samu canjin yanayi, can gidan su mama

kuwa ba kowa, ba za mu ji dadin zama ba shi ya sa

muka taho nan ko ba komai za ka debe wa yara

kewar babansu.

*My dear, bathroom is ready,

Misbah ta iSO

falon tana fadi, ka san yau gajiyar da muka kwasa

daban ce, kana bukatar wanka da kwanciya da

wuri, don samun hutu, nan ta ja hannunsa suka

fice.

Farida ranta ya mummunan baci, ta ji tamkar ta www.dailynovels.com.ng

rufe Bahijja da mari, wai ita waye da ta isa ta shiga

tsakaninta da Deeni, wai ta san ya suke da Deeni

kuwa, tsintacciyar mage mara asali za ta nemi nuna

mata gadara.

“Baki isa ba Bahijja sai na kwato matsayina da

kika kwace a gurin iyayen Deeni, ‘yan’uwansa da

kuma zuri’ar Deeni, dukkansu nawa ne ba naki ba,

za ki koma inda kika fito, na yi maki wannan

alkawarin.”

Nan da nan ta nufi kujera ta harde kafa daya kan

daya, zuciyarta na huci tana tafasa, yara ko suna ta

tsalle-tsallensu, in sun gaji su kalli cartoon, Baba

Audi nata hidima da su, duk abin da suka nema ta

kawo masu, da ma ita gwana ce wurin harkar yara,

Bahijja ce ta leko ta kwala wa Zulai Kira, ta taho

kayan su Farida, ta ce ta dauka su nufi

bangaren baki, wanda kwata-kwata ba hade yake

da bangarensu ba ma. Zulai na rike da kayan

Farida, Bahijja kuwa da na su Deeni karami ta ce,

“Yara ku zo mu je inda za ku kalli cartoon, yadda

kuke so, don a nan in uncle Deeni ya fito, kashewa

zai yi, ya kunna labaru, can kuwa inda kuke so nan

za ku kalla, kun san akwai chocolate, ice-cream

kala-kala da biscuit a wurin specially for you yara

irinku irinku in sun z0.

Yee! Suka tashi suna

tsalle. Suka bi ta, ta kalli Farida ta yi mumushi ta

ce.

” Aunty Farida ko, za mu je ki ga masaukinku, in

ya so sai ki dawo, in Kina da bukatar hira a nan,

murmushin dole ta yi ta mike.

Ta bi ta bangaren da ta kai su, wuri ne mai

kyau, ba abin da babu a ciki na jin dadin rayuwa, www.dailynovels.com.ng

masaukin baki ne na musamman, saboda ba Farida

ba ma Bahijja a tsarinta bata yarda, wani ko wata

su yi masauki a bangarenta da Deeni ba, saboda

tana ga wannan sirrinsu ne, wurin da suke gudanar

da rayuwa daga ita sai shi, wannan tsarinsu ne,

tunda Allah ya azurta su da in da za su ajiye wasu.

Kuma duk abin da suke bukata akwai shi wurin,

gida daya ne amma sai an fita daga wannan

bangaren sannan a je wancan.

Lokacin da suka isa Bahijja ta kai wa Farida

kayanta daya dakin, yayin da na su Deeni karami,

daya dakin wanda suna ko kallon juna kowane daki

da bayinsa ciki, sai falo mai matsakaicin girma,

hatta kicin akwai a wurin. Bahijja ta kalli Farida ta

ce,

“‘ina ga kamar za ki fi sakewa ku huta da kyau a

nan, saboda sirri yana da dadi privacy musamman

macen da ta yi zama a gidan aure, gidan kanta,

wani kaddaran ya raba ta da auren, to ina ga zama

tare da wasu ko dakin wasu in ba ya zama dole ba,

zai zame mata matsi da takura, amma kin ga a nan

za ki sake tamkar yadda kike da bangarenki a

Kaduna.” www.dailynovels.com.ng

“Haka yara ma zabin ki ne ki kasance da su ko

ki bar su a nasu dakin duk abin da kuke so kuke

bukata za ku same shi. in hira ce ma kuna iya zuwa

ciki in muna nan ayi hira in an watse kowa ya

koma masaukinsa, na ji kin zo rubuta Jamb ko?

Allah bada sa’a, na ga dare ya yi, ina ga da ma

kuna bukatar hutun kamar yadda muke bukata, don

haka sai da safe.

Faridan ta yi murmushin yake wanda ya fi kuka

ciwo, tace na gode da addu’arki da karramawarki

gaskiya ne zan fi son zama a nawa dakin da

bangaren fiye da naki.”

nan suka kalli juna ido

cikin ido, alamar dukkansu sun fahimci sakon da

suke ba wa juna a fakaice. Farida ta fahimci

Bahijja na son nesanta ta da mijinta ko ta halin

kaka, yayin da Bahijja ta fahimci tana son shigowa

cikin gidanta da rayuwar mijinta kota halin kaka.

wanda lokaci ne zai muna, mai nasara cikinsu, Nan

suka yi wa juna sai da safe, Bahijja ta juya ta fita,

Farida ta bi ta da kallo ta ce,

“kwarai bangarena da

dakina nake nema da kuma masoyina da kika

kwace min matsayin mijina.

Bahijja ta samu Deeni a bayi kwance cikin

Jacuzzi idonsa rufe duk da yana jin dadim ruwan

yadda yake ratsa shi, yana gasa shi da tausar jikinsa www.dailynovels.com.ng

amma wanna bai ba shi kwanciyar hankali da natsuwar da yake bukata ba, abubuwa da yawa ke

yaw cikin kwakwalwarsa.

Shin taya zai soma bullo wa wannan sabuwar

fitinar da tashin hankalin da suka kunno cikin

gidansa da rayuwarsa, ya san halin Bahijja zai

share a komai a gunta amma banda wannan, dan

zai iya kiran wanna karon shi ne tashin hankali da

sabani mai tsanani tsakaninsu tun aurensu, kansa

ya dau zafi sosai, ya ji motsin shigowar Bahijja

tana daure da towel ta tufke gashin kanta, ya zura

mata ido yana kallonta cike da so da sha’ awa, tana

tafiya tana yauki takun isa da jin a daidai take,

jikinta sai kadawa yake kamar reshe, tana juya

manyan idanunta dake kunshe da abubuwa kala-

kala sai da ta iso daf da shi ya dage idonsa da kansa

daga gareta.

Zama tayi gefensa yayinda ta sa hannayenta

cikin ruwan tare da shafar bayansa da masa matsa

da tattausan yatsunta bata ce mai kala ba, sai

lumshe ido ya yi yana jin dadin hakan da wani irin

sukuni a zuciyarsa da jikinsa gaba daya, hakika ya

yarda Bahijja ita ce farin cikinsa da kwanciyar

hankalinsa da duk wani sukuni nashi, Bahijja

natsuwa ce sosai a tare da shi. Can ya ji ta shigo

cikin ruwan ita ma ta kwanta a jikinshi suna gogar

juna ta kwantar da kanta bisa kirjinsa, ta ji sonsa na

ratsa zuciyarta, da ruhinta yayin da take jin bazata

taba iya rayuwa da wani namiji ba sai shi, haka nan

tsananin kishin Farida ta ji yana cin ta a ranta cikin

HMMM LABARI FA NATA TAFIYA SHIN KOYA ZATACI GABA DA KAYAWA KUDAI KUCI GABA DA KASANCEWA DAMU A KODA YAUSHE

www.dailynovels.com.ng

Related Articles

Leave a Reply

Check Also
Close
Back to top button

You cannot copy content of this page

Adblock Detected

YOU ARE USING ADBLOCK TURN IT OFF TO COUNTIUE BROWSING OUR WEBSITE