MISBAH BOOK 3 CHAPTER 9 BY SA’ADATU WAZIRI GOBE

MISBAH BOOK 3 CHAPTER 9 BY SA’ADATU WAZIRI GOBE

 

 

tsakaninsa da Misbah ba ko da kuwa Farida ne,

Misbah sirrinsa ce, haka kuma shi sirrinta ne* ba mutum na uku da zai taba shigowa tsakaninsu ya san wannan sirrin.

Wucewa ya yi kai tsaye dakin ya murda kofar yaji ta a garkame, tabbas ya san akwai tsiya

tsakaninsa da Bahijja. Kyaleta ya yi ya ba ta lokaci

zuwa wayewar gari, idan ta huce zai mata bayani

su fahimci juna, wannan ne dare na farko da suka

taba raba wurin kwana, a wannan daren dukkansu

sun kwana da zugin zuciya. Deeni

ya dinga

mamaki da tunanin irin yadda Farida ta sáuya

wadda sam da ba hakan take ba, tana son kutsowa;

cikin rayuwarsa,

ta wargaza masa

gida• da kwanciyar hankalin da ya samu, ta fi kowa sanin

cewa shi mata biyu ba ra’ ayinsa ba ne, mace dayan

nan ta ishe shi rayuwar aure, Bahijja kuwa it ce

abokiyar rayuwar da Allah ya zaba masa wadda

rayuwarsu da tunaninsu suka zo daya, Allah ya

masa sauyi na alkhairi.

“Haka nan yadda Bahijja

ta rike nida

muhimmanci da amana, ta sadaukar da rayuwarta,a

kaina, ta rike ni ta kula dani, ta fahimce ni, ta

fahimci yanayin rayuwata da tunannina, ta bani

goyon baya, ta ba ni nitsuwa da kwanciyar hankali

har na samu abin da nake so a rayuwa, na sha shiga

hakkinta da lokacinta saboda burina da ayyukana* a

rayuwa, akwai kyakkyawar fahimta da sadaukarwa

a tsakaninmu, ina alfahari da mace irinta kuma zan

kare mata hakkinta da mutuncinta da farin cikinta,

na fahimci kishinta ga Farida shi ya sa ma banga

laifinta ba, saboda wannan ne karo na farko da

muka samu mummunan rashin fahimta, amma

insha Allah komai zai daidaita kamar kullum

please Bahijja yanzu ma ki fahimce ni

Da irin wannan tunane-tunanen ya kwana har

asuba, ya nufi masallaci, ya dawo amma har yanzu

ba ta bude kofar ba, ya buga ya yi magana shiru har

ya ji ransa ya fara baci, wannan zuciyar ya ji tana

taso masa amma ya yi kokarin danne taya nufi

dakinsa ya dauki ¡pad dinsa yana latse-latse, amma

abin ya gagara, bacin ransa sai karuwa yake,

zuciyarsa nata saka masa tsiya da arziki duka.

A bangaren Bahijja kuwa har yanzun tana cikin

zafi, ba ta so su yi ido biyu da Deeni, su yi sa in-sa

da, zai sa su tunzura juna har ya jawo wani

mummunan fada tsakanin su, zbacin ran miji ga matarsa ba karamin

masifa ne a gareta ba, da haka ta gwammace su bawa juna lokaci.

Farida kuwa ba sallama ba shiri ta tattara

yaranta ta tafi, sai da ta zo shiga jirgi tayi wa

Deeni text cewa ta tafi a yanzu, amma domin tadawo gaba daya, ya fada wa Bahijja kar tayi dogon

farin ciki, tana nan dawowa gaba daya, idan na dawo gidanka a matsayin matarka Deeni, zan cire

maka aljannun Bahijja da suka mantar da kai

shaukinmu da soyayyarmu, zan tado maka da

tsohuwar soyayya da tsohon alkawarin da ke

tsakaninmu zai cika

Tsaki yayi ya kashe wayar, yayi wurgi da

wayar, ya tashi ya yi wanka, duk da Lahadi ne bai

zuwa gidan gonarsa, sai bayan azahar ko da

yamma, yakan zauna da Misbah su tattauna

matsalolinsu, su kasance tare da juna a wannan

ranaku na Asabar da Lahadi, sai dai fa in lokacin

Fitarsa gidan, dan haka a tsarinsa Asabar da Lahadi

Yana fita ne tsakanin azahar zuwa la’ asar, amma a

wannan haka ya fita da safe ba shiri, dan a can ne

Yake ga zai iya samun sukuni da natsuwa. Jin

fitarsa ya sa Bahijja ta tashi ta yi wanka ta sa wani

abu a cikinta, ta shirya ta duba agogo karfe goma

na safè ta fito ta yi tunanin za ta samu su Farida sai

ta tarar ba sa nan, Baba Andi ke Fada mata sun tafi

tun karfe bakwai na safe, ta yi shiru na dan gajeren

lokaci, sannan ta ce,

“Baba Audi zan wuce asibiti,

ni ma zan leka ban jin dadin jikina, in na fita ina ga

zan dan warware, sai ku shirya abincin rana kafin

in dawo, sai mu yi na maigidan tare.” “To Hajiya,

ta amsa ta yi ciki. Har ta fita sai ta dawo ta leka

bangarensa, daki da falon ta tattara ta gyara tar da

wanke masa bayi, duk da ba wani datti amma

ka^ida ne kullum sai ta wanke, ta jima tana tsaye

tana kallon dakin, irin rayuwar da suke gudanarwa

ciki mai dadi da marar dadi, ba su taba raba kwana

ba, wannan ne karo na farko, haka ta ji abin yana

matukar mata ciwo, zuciyarta na mata zali, tayi

saurin fita ta rufe wurin ta nufi asibiti, ta bi tana

leka marasa lafiya sama-sama ita ma dai Lahadin

bata fita sai da yamma bayan litar Deeni, in ba dai

emergency ba ne.

Su kansu ma’aikatan sunyi mamakin ganinta a

lokacin da ba su saba ganin ta ba, saboda sun san rayuwar

Dr. Bahijja akwai ka ida,

duk iya

kokarinta ta samun sukuni ta kasa, dan haka ta bar

cikin asibitin ta nufi gidanta dake wurin ta bude ta

shiga ta nufi Study room dinta kai tsaye tare da

dauko wasu littatafai da take ganin in ta karanta za

ta samu sauki do ‘Not be Sad shine littafin da

kullum take karantawa inta tsinci kanta a cikin

wanna yanayi wanda wani shahararren malamin

Addini dake Saudi Arabia ya rubuta shi, inda ya ba

da misaliai da hadisai da ayoyi tare da rayuwar

magabata annabawa da sahabbai

Tabbas wannan littafi ba karamin kore mata

kewa da damuwa yake ba, ta nutsu sosai cikin

karatun, duk da ta gama littafin, amma kullum in

tana karanta shi sabo yake zama mata, tayi nisa

sosai, tana ji yana ratsa ta ba ta ankara ba sai ji ta yi

an waino kujeran da take zaune, an juyo da ita,

Deeni gaban ta, ya sa kafa ya take kujeran ya

sunkuya gabanta ya ce,

“Ganin matar nawa ko sai

na yanki ticket ne an ba ni lasisin ganinta? Nan tayi kokarin danne zuciyarta ta yi murmushin dake

kara wa fuskarta kyau tace,

“wa ya isa ya yanka

wa miji ticket din ganin matarsa? ai wannan

mallakina ne Allah ya ba shi, halak malak, sai

yadda ya yi da ita.

Ya zuba mata ido “ban ga alamar haka daga

tawa matar ba

“Anya kuwa Deeni ka sake ware idanu ka duba

da kyau, matarka ba ta taba sanya hijabi a

tsakaninku, bata ta ba ba wa wani abu muhimmanci fiye da mijinta ba, in ba bautar Ubangijinta ba.Shi ya sa jiya kika rufe min kofa? Ko mai hakan

yake nufi?”

Ta kau da kai tare da fadin “Rufe kofar yafi

bude ta alkhairi saboda idan na bude ina cikin zafin

zuciya da bacin rai komai na iya fadi wanda hakan

zai iya jawo min fushin Mahaliccina.”

“Kina tsammanin matakin da kika dauka na rufe

wa mijinki kofa Allah ba zai yi fushi da ke ba?”

Ta mike tana kallon shi yana kallon ta, ta ce,

“na ji, nayi laifi, ina neman ka yafe min laifin da

na yi maka.” Tana fadi ta wuce ta fara tafiya, ya kira sunan ta

“Bahijja. Ta tsaya, can ya sha gabanta

tare da harde hannun, zuciyarsa na masa zafi ya ce,

“‘wai me kike ji da shine? me kika dauki kanki? na lura da wasu halayye da kika fitar da su wanda ba haka na sanki da su ba,

” ta ba shi amsa da cewa,

“kamar yadda ka dinga fitar min da wasu halayya

da ban san ka da su ba, ko ni ba mutum ba ce? ko

ni ba ni da zuciya ba ni da feelings din da zan ji

zafi? Kina nufin yayan Yaya Shamsu ko Farida basu isa su zo gidana ba, ban isa in yi magana da Farida ba saboda ke ba kya so? to, ni ba na daya

daga cikin mazajen da matayensu ke juyawa,

komai kuwa son da nake maki ba za ki sa in

HMMM LABARI FA NATA TAFIYA SHIN KOYA ZATACI GABA DA KAYAWA KUDAI KUCI GABA DA KASANCEWA DAMU A KODA YAUSHE

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button

You cannot copy content of this page

Adblock Detected

YOU ARE USING ADBLOCK TURN IT OFF TO COUNTIUE BROWSING OUR WEBSITE