MUSAYAR ZUCIYA CHAPTER 20

MUSAYAR ZUCIYA 
CHAPTER 20
Around 1:45am Abubakar ya shiga cikin gidan nasa bayan ya gama kulle ko’ina yana son lekawa yaga yasuke amma yana tsoran yadda zai shiga ya gansu dan yasan matan kauye basu fiye kwanciya da riguna ba dan haka ya koma yashiga dakinsa ya kulle. ‘ Wayar INdo ya dinga kira amma ba’a daga ba ya ajiye tare da shiga wanka. Sukuwa su 
INdo bayan an kawota tafita suka zagaya gidan farin cikinta ya kasa boyuwa ganin irin 
gidan da take ciki gida irinna cikin films hadadde wanda ko cikin mafarkinta bata taba zaton zata taba koda jikin gidan ba, tun shadayan dare suka barbaje bayan sunci sunyi hani’an ga iskar fanka na kada su ai babu wanda ya kuma motsawa munshari kawai kakeji yana fita hahhhussss ta kowace kusurwa. a Tun sallar asuba yafita, su kuma suna tashi suka hau shirin tafiya, saida yaje gida yasa Mama ta bada abinci aka kaimusu sukaci wajan karfe goma na safe ya kawo musu buses biyu ya biya masu motar sannan suka tafi sunata yiwa lNdo Allah sanya alheri. Saida yaga sun tafi sannan ya shiga gidan, a tsaye ya tarar da INdo tana wajan dining bakinta a bude sai shafar kujerun takeyi ya tsaya yana kallonta ba tare da tasan yana tsaye ba. 
Yana kallonta ta dan dosana duwawunta akan kujerar sai kuma tayi saurin mikewa tana dariya tana karkade gurin, ya shigo a hankali cikin rashin sa,a ta hangosa ta cikin glass din drawer flats na dining dake wajan. Da sauri tayi hanyar shiga daki zata gudu yayi saurin cafko ta yana dariya yasanya ta a jikinsa. 
Fisgar jikinta takeyi zata gudu amma ya hana hakan faruwa, kanshi ya zura a wuyanta ya fara shin-shina wuyanta yana sanya siririn hancinsa cikin kunnanta iskah na shiga ciki, lNdo taji wani irin abu hankalinta ya fara tashi kwakwalwarta ta fara aika mata da wasu bakwannin al’amra.Jin hannunsa a kan kirjinta ne yasata kwallara mai wata uwar kara, Abubakar yaki sakinta saima jikin bangon kofar da zata kaita bedroom dinta ya jinginar da ita gaba daya ta tsure ya kamo fuskarta da duka hannunsa biyu, bakinsa yakai saitin nata zaiyi kissing dinshi INdo ta kwalalo mai ido tana bin harshensa da kallo tamkar idonta zai fado sai girgiza kai take alamar bata so. 
Ganin kamar abinda yake shirin yi mata ne bata so yasa shi sonyi mata dan ta gane cewar ba wani abun aibu bane. Gate yajiyo ana bugawa nan lNdo ta fara sauke numfashi dan tasan dole yanzu yaje ya bude, ba zato bare tsammani kawai taji ya zura mata tongue dinsa tayi-tayi ta datsa bakin amma ta kasa ya fara tsotsa ‘tare da zame dankwalin kanta yana shafar gashinta. Nan da nanjikin lNdo ya fara kyarma tamkar shocking yajata yayi kokarin tattarota zuwa jikinsa still mouth nasa na cikin nata idanunta a ‘tamke ta dunkule hannayanta jira kawai takeyi taji zubar fitsari. Sake bugun gate d’in ake da karfl amma yaki kulawa hankalin lNdo ya kuma tashi, sai da yayi mata ya tabbar da sakon salonsa na farko ya shigeta sannan ya cikata aikuwa ta zandama daki da gudu hartana bugewa da bango yayi dariya yana kallonta harta shige sannan ya gyara wuyan rigarsa ya fita yana budewa yaga sisters din Mamansu ne da yaransu ya fara sosa keya aunty Shafa’atu ta kallesa dakyau sannan tace. “Doctor ko baku tashi bane ba tun dazu sai faman bugu mukeyi..?!” “Ah mun tashi mana aunty yanzu ma na koma ciki da ‘yan uwan Humairan suka tafi.” 
“Oho toh.” Suka fada tare da shiga ciki suna kiran sunan lNdo. 
Shiru tanajin su taki fitowa sabida gani takeyi kamar idan ta fito zasu gane, yana zaune a gurinsu yaga taki fitowa yasan dalili hakan yasa shice musu yana zuwa. Kwance ya ganta kan gado ta yaye bedsheet din ta cukwikuye jikinta gabaki daya ta kudindine ya tura dakin yana murmushi da mamaki ya hau kan gadon. Qarah curewa tayi Abubakar ya janyota gaba dayanta ya fara warware bedsheet din amma sai sake nadewa take cikin kasalalliyar murya domin wannan kokawarda sukayi wani shauki ne ya dinga saukar mai yace mata a hankali. “Please Humairah tashi kizo muje sisters din Mama ne suka zo, bana son naji sun fara yin korafi dake kinji…?!” Tana cikin zanin gadon tace mai. “Toh amma kuma saika fita..” “Toh nafita kizo yanzo sai ki kawo musu lemo da ruwa.” Yana fada ya fita daga dakin sai dai yana labe, tashi tayi ta sakko a hankali ta karasa gurin madubi tana shafa bakinta ta kuma budesa ta kallesa a cikin madubin a fili tace. “Kai likita da kazanta kake wallahi irin na film yayi min, amma fa kamar da dadi hi har wani lumshe ido yake yi.”Dariya ce ta kusa tona mai asiri hakan yasa shi juyawa ya fita falon yana yi gashi ya kasa denawa mutanen dake falon suka bishi da kallo suma suna murmushin kowa da abinda yake kisamawa wanda yasa shi dariyan. 
“Abin na masoya ne me ta gaya maka haka kake babbaka dariya.” 
Shafa keya yayi yana shirin yin magana saiga INdo ta fito hannunta a saman bakinta sai faman rarraba idanuwa takeyi aunty Siyama tace. “Aunty amarya taho nan ki zauna.”A dardar taje ta zauna kafin ta fara gaidasu kananun kuma suka gaida ita, hada ido suka yi da Abubakar yayi mata alamar ta kawo ruwa cikin sa’a ta mike taje inda taga an ajiye lemukan da ruwan ta dauko ta kawo da yawa sannan ta koma zata zauna Abubakar yace. 
“Hunairah baki d’akko musu kofina ba.” “Au dan Allah kuyi hakuri kunji bari na dakko.” Ta fada tare da shiga tsalelen kitchen dinta, kalle kalle ta farayi domin gabaki daya ta hargitse ta shagala da kallon dukiyarda aka kashe harta manta da cewar aikota akayi. Itace taba nan shafa can shinshina nan haka ta dinga yi, shirun dayaji ne yasa shi mikewa yabiyo bayanta. Tsaye ya tarar da ita tana taba electric oven taga hotan kaza ajiki ya bita da kallo, sam baya ganin aibunta domin yasan dole tayi haka tunda ba ko ina akeda irin abubuwan ba dan ko gidansu Abubakar din babu wasu abubuwan da ya zubawa INdo. Karasawa yayi ta kallesa tare dajuya Mai baya yayi dariya yace. “Ohh su Humayrah daga zuwa dakko cups sai mukaji shiru.” 
“Lah wallahi mantawa nayi bari na kaimusu, amma wanne zan dauka..?!” Ta fad’a ba tare da tajuyo ba, ya karasa tare da janyota jikinsa yace, “Kibar shi sunma farasha dajarkar.” 
Toh sakarni na fita gurin su.” 
Naki din da wayace kiki komawa..?!” Jin ya fara shafar jikinta ne yasa ta faraturesa ya juyo da ita ta kawar dakai sai ji tayi bakinsa a saman kirjinta INdo ta zabura ya saketa ta ruga falo nan ma suka bisu da kallo ita dai lNdo harta zauna jikinta be dena rawa ba a haka har suka gama zamansu sukayi musu fatan zama lafiya sannan suka fita suna tafiya wasu suka zo ranar ma dai haka suka wuni da baki. Misalin k’arfe goma na dare Abubakar ya shigo gidan, tsit ba kowa sai karar inji ya rufe ko’ina sannan ya shiga falon, zaune ya ganta tana kallo ta kurawa TV din ido sai dariya takeyi da alama film din yayi mata kyau. Duk sallamar da yakeyi bataji ba sai daya shigo har tsakiyar falon ya kare mata TV din sannan taganshi tana dariya tace. “Kai dacta dan Allah ka matsa kana kare min.” Hannu ya bude mata alamar tazo suyi hugging amman taki sai ya kashe kayan kallon gabaki daya tare da karasawa dining ya ajiye ledojin hannunsa. Tashi tayi tana turo baki ganin ya kashe mata gashi bata iya kunnawa ba dama su Hawwa ne suka kunna dasuka zo ya juyo ya kalleta tare da cewa. 
“Kin manta k0, da bakinki kika cemin malama ta baku labarin matarda bata bin umarnin miji da abinda akayi mata ko? Shine yanzu nace kizo kiyi min oyo-yo kikaki ba ruwana dake? INdo ta tuna tayi saurin zuwa gurinsa ta tsaya, ganin haka yasa shi kuma ware mata hannunsa a hankali ta shige bayan ta rintsa idanuwanta ya rungumeta shima. A saitin kunnanta ya tambayeta. “Kinyi sallah..?” 
 Kada kai kurum tayi sannan nan yace. “Zo muje muyi wata muyi addu’a alkairin dake cikin auran mu Allah ya tabbatar dashi.” Tunawa lNdo tayi da labarin dasu Uwani suka bata cewar indai taji miji yace ayi sallah akuma ci nama toh ranar aikwai aiki musamman ranar da aka kaika. Janta yayi suka nufi bedroom dinsa dama bata taba shiga ba, taga wani shegen gado me shegen kyau bakin ta yaki rufuwa yace. “Zokije kiyi alwala.” Tace “Dacta tsaya na gama ganin gadonka wallahi yayi kyau Allah sanya alheri.” “Amin Humaira amma ai shima nakine, duk abinda kika gani na gidan nan nakine ko mutuwa nayi baza a raba gadona dasu ba.” Cikin tsananin murna INdo tace tana kallonsa. “Dacta da gaske kake nawane.?!” Kai ya daga mata ta fara murna tana godiya sannan ta shiga bayin tayi alwala, tana fitowa shima yayi lokacin ta dawo daga dakko hijjab, karba yayi ya bata sabo tasa sannan yajasu sukayi 2raka’at sannan ya dafa kanta yayi mata addu’a suka shafa. Hannunta ya kama suka koma falo ya kunna musu kallo suna dining suna kallo ya dinga feeding dinta sai da taci ta koshi ta kora da madara sannan tace ta koshi. “ 12:45am suka shiga dakinsa INdo sai hamma takeyi najin bacci, saida ya hada mata ruwa tayi wanka sannan shima ya shiga ya fito sanye da boxer tayi saurin kawar dakai tana zaro ido gashi ya kulle dakin itama daga ita sai towel ya kwashe mata kayan ta nema ta rasa. Turare ya shafa kawai sai na mouth sannan ya nufi gurinta dasu,zama yayi a kusa da ita tayi saurin matsawa shima ya matsa tare da rikota da sauri tace. “Na higa uku ni lNdo dan Allah dacta kayi hakuri.“ “Shhhh.” Yayi mata tare da matsa mata turaren yace ta bude bakin ya fesa mata da sauri ta tufar da yawu a kasan bedside carpet yace. 
“Humaira ya haka.?!” INdo kamar tayi kuka tace “yo toh ai ba dadi.” Dariya yayi tare da girgiza kai sannan ya tashi ya mayar tare da dakko handkerchief ya goge gurin. Light off yayi musu sannan ya kuma kunna bedside lamp bulb din green light ya haske dakin yayi kyau lNdo ta kalli dakin ta kuma sakin murmushi ita dai yau tana ganin ikon Allah a gidannan. A hankali ya sargafota ta fara zillo towel ya fara kwancewa tace. 
Wai kai bazan sa kaya bane.?” a 
Cikin sanyin murya Abubakar yace “Eh a haka zaki kwana ko kina son nace bana so amma kuma kisa…?” Ya tambaya yana shafa gashinta, wani yawu ta had’iya tana kada kai, ya janyota kan gadon towel din ya yaye daga kasa lNdo ta saki kara jikinta na rawa. A hankali ya kuma jantajikinsa sannan ya zare mata towel din gabaki daya ai INdo sai kuka tana cewa. “Yaya Abbakar karka kalleni in kanawa iyayenka, ni wallahi ka dena tabani banasan 
iskanci…” Sam bazai iya yi mata abinda takeso ba, shi amatsayinsa na likita yasan idan ya barta besamu nutsuwa ba zai shiga tashin hankali ya kuma San akwai illah hakan. A hankali cikin wayewa da iya ‘TATTALIN MACE’ Abubakar ya dinga tunatar da ita yana kuma nuna mata illar hanashin da takeyi a haka ya samu INdo ta yadda dashi ta bashi kanta duk da tasha 
kuka hardasu majina. Yana daga kwancen yace, “Ohh so sorry my wife, please zoki rama kema.” 
Tana kukan ta kasa-kasa tace. 
Meh zan rama..?!” Ai Abubakar besan lokacin daya kyalkyale da dariya ba haushi ya sake zuwar ma INdo ta juya ta fara dukansa yana karewa da hannu… 
Hmmm dacta habubakar dai ya cika buri indonsa kuma an zama cikakkiyar mace😉

Related Articles

Leave a Reply

Check Also
Close
Back to top button

You cannot copy content of this page

Adblock Detected

YOU ARE USING ADBLOCK TURN IT OFF TO COUNTIUE BROWSING OUR WEBSITE