RANA DAYA BOOK 2 CHAPTER 15

RANA DAYA BOOK 2 CHAPTER 15

 

 

Ta nufi cikin gidan jiki a sanyaye, kasa bude

fofarta tayi. Tabi motar da kallo har ta tsaya a

cikin jerin motocin Amna da Shatima. Ta bude

kofar ta ta shiga. Kasa cire kayan Makarantar

tayi, haka kuma ta kasa dora girki, duk ga kayan

Cefanen a gabanta. Ta dai yi ta maza ta kunna

Risho ta dora tafasasshen nama.

“*Lokacin da su Hajiya suka shiga gurin Nafisa

tana wanka. Hamida ta yiwa Mama da Hajiya

oyoyo. Aliya ta ga shigar mota, kuma ta leko taga http://WWW.DAILYNOVELS.COM.NG

bakin Nafisa ne, don haka ta yafa mayafi ta fita

zata je da sigar duba jiki.

Tana shiga taga su Hajiya, gabanta ya fadì don

tasan Hajiya ba kalar wasa ba ce Amma duk da

haka ta cije  ta isa ta zube gwiwa biyu a gaban su

tana gaishe su, yanda kasan zata yi musu sujjada

don girmamawa.

Hamida ta aje musu ruwa da lemo. Aliya ta ce

“‘Hamida ya jikin Nafisar? Yau da dadì jikin ko?”

Hamida ta CE

“Eh, gata can ciki tana wanka.”

Cikin kissa ta ce

“‘Masha Allah, kai naji dadi,

amma ta sha magungunanta ko?”

Ta ce,

“Kin san sai kin zo zata sha, don nayi-

nayi ta ki sha.

Aliya ta Ce

“Bari ta fito sai in

lallabeta ta sha. Naso in yi mata faten tsaki yau

ban san inda zan samu tsakin ba ne, amma ga

Rama can Maigadi ya siyo min.

Duk zubar da take yi su Hajiya suma jin ta,

kuma sun yaba mata musamman Mahaifiyar

Nafisa, don an ce me da wawa. Maman ta ce,

“Allah http://WWW.DAILYNOVELS.COM.NG

Sarki, kina ta dawainiya ko, kullum

Hamida tana fada min komai dare sai kin fito kin

dubata.

Hajiya ta ce, “Ai haka ake so shine zaman tare,

bare dama haka ake son babba. Ina ita “‘yar uwarku

fa?”Aliya ta ce,

‘”Amna, tana gurinta. Ita kuma da

sauki, sai bacci amma bari in dubota nasan yanzu

ta tashi.”

Mama ta ce,

“Allah Sarki, kiyi dawainiya da

wannan kiyi da waccan, Allah yayi miki albarka.

Aliya ta ce,

“Amin Mama.”

Ta fita cikin jin dadì

ta nufi sashen Amna ita dama burinta ta shiga

gurin kowa a yarda da ita, haka zai bata damar

kunna duk irin wutar da ta so.

Ta samu Amna zaune tana kallon TV, me

aikinta kuma tana bare mata Kwai guda biyu a kan

plate. Ta ce

“Sannu da hutawa.

.” Kallo daya Amna

tayi mata, sannan ta ce,

“Yauwa.

.” Ta maida kanta

gurin TV

Aliya ta ce “Hajiyar Shatima ta z0 tana dakin

Nafisa, ta ce in zo in kira ki.

Amna ta ce.

“Ina zuWa.

Aliya ta fita. Amna taja tsaki, “Ban da

Hajiya ce babu dakin wadda zan je. Itama Hajiyar

ta sauka can ne don ta nuna cewa tafi son

“Yar uwarsu, kowa Nafisa! Nafisa!!”

Aliya tana fita dakin Salma ta nufa, ta same ta

tana jajjage. Ta ce

“Ga su Hajiyar Shatima can

kije ki gaida su da Maman Shatima.

Salma tayi http://WWW.DAILYNOVELS.COM.NG

rau-rau cikin tsoro, ta ce “Anty wallahi tsoro nikeji.”

“Tsoran wa?” Salma ta ce,

“Hajiya, wallahi,

Aliya ta ce, “Sai ka ce wata Mayya! Ta haifa miki

mijin ga shi nan yana ta uban kashe miki kudi

amma ki ce kina jin tsoronta?”

Salma ta ce,

“Ba haka ba ne Anty, ta taba yi

min fada ne, kuma ni tsoron fada gare ni.

Tayi

murmushin mugunta, a ranta ta ce,

*Yanzun ma

wani fadan zan sake ja miki.

* Ta dubi Salman.

“Wuce kije ki gaida ta.

Salma ta CE

“Bari in canza kaya, in cire na

Makaranta.

Aliya ta yatsina fuska jin cewa Salma

Zata cire kaya, in ta cire ai ta rage mata saukin da

ta samu na tseguntawa Hajiyar irin kudin da

Shatima ke kashewa Salma, wanda

abin ke

damunta kullum.

Salma ta dauki dan mayafin jallabiyarta ta

yafa, tunda kanta babu dankwali. Ta fita cikin

fargaba ta nufi sashen Nafisa. Aliya ta shiga

dakinta, dama ranar ita ce da Shatima, kuma ta

shirya masa farfesun kaza, yana wuta ma bata

gama ba.

Sannan tayi dafa-dukan kus-kus da hanta, nan

ta jero ma su Hajiya katon tire. Ta shigo dakin

Nafisa. Ta samu Salma tana rabe ta kasa karasawa ciki. Har da tsawarta “Mu je mana kin wani rabe.

Hajiya ta ce, “Wace ce?”

Aliya cikin sigar son

tura Kiyayyar Salma ga surukar tasu ta ce,

“Salma ce uwar shashanci.

Hajiya ta gimtse fuska har

Amna da Mama dake zaune. Salma ta tsugunna a

gabansu, kana kallonta ka san a firgice take.

Aliya ta dire tiren a gabansu nan kamshi ya

cika dakin. Ta kalli Hamida

“Kawo plate da http://WWW.DAILYNOVELS.COM.NG

cokula.

Salma cikin raunanniyar murya ta ce,

“Sannunku da zuwa Hajiya.

Mama ce ta amsa

“Yauwa sannu yarinya.” Ta kalli Nafisa wadda ke

Taune kan kujera ta ce,

“Sannu Anty, ya jiki?”

Itama fuska tam! Ta ce

“Da sauki.

Ita kowa ya saka ma ido. Hajiya ta kalli Salma

cike da tsana. Ta ce, “Haka ne? kudin makarantar

dubu saba’ in da biyar?”

Salma cikin rawar jiki ta

ce, “Yanzun sun cike tamanin.

Hajiya ta mike cikin sauri,

“Kice ke ya ke yi

ma aikin kenan? Kullum ta Allah dubu da dari

biyar a wata nawa kenan? Jama”a kuyi min

lissafi.

Amna ta cE

“Dubu arba’ in da biyar.

* Nafisa taCE

“Kan uba! Muna zaune?”

Hajiya ta ce,

“To al

ko ni da na haife shi ya min haka nasan ya kai da.”

Maman Nafisa ta ce

“To shi me ya kai shi wannan

batan basira? Wai rokon Allah da goge.”

Hajiya ta soma kiran layin shi ya daga. Ta ce,

“Ina gidanka, Allah Yasa ka kusa tashi?” Ya ce,

“‘Insha Allah nan da awa daya zan dawo.”

Ta cE

“To sai ka iso.

Ya ce Ke da wane ne?” Ta ce,

“Ni da Mamanku ne, Mustapha ya kawo mu

Salma wadda sautin kukanta ya soma fitowa tace, “Don Allah Hajiya kuyi ha…

‘ Jifan da Hajiyar

tayi mata da dan karamin filon kan kujerar ne ya

hanata karasa maganar. Hajiyar taci gaba da cewa,

“‘Ban son jin komai daga gare ki ‘yar dangin masu asiri

Ai tun daga kan yanda yaron nan ya zo tamkar

ya yi hauka a kan wannan kazamar nasan aikin

sihiri ne.” Ta kalli Maman su Nafisa.

“Ki tuna fa http://WWW.DAILYNOVELS.COM.NG

bai taba kwanciyar asibiti ba sai a silanta, dan na ce

ba za ya aure ta ba, ranar ya tashi a sankare idanu

kakkafe muka nufi asibiti.

Duk matan suka kalli Salma cikin mamaki,

musamman Amna wadda take da matukar tsoron

asiri. Na fisa ta ce,

“Wai dama ciwon nan saboda

ita ya yi?”

“Hajiya ta ce,

“‘In kin je gaba ma ki fada.

Da naga abin nashi yayi yawa, sai nasa a yo min

tambaya gurin Malamai, can suka fada min uwarta

tasa an yi asiri da sunan Shatima, kuma an hada da

naman bakar Akuya da miyon bakinta da ruwan

hawayenta an ba shi ya ci. Daf da bikin fa har gida

ya sai musu.

Cikin sauri ta dago tana fadin “Wallahi haya

ce.

Hajiyar ta sake jifanta da wayarta da ke

hannunta.

“‘Karya zan yi miki don ubanki?”

Aliya cikin sauti ta dauki wayar tar da fadin,

“Hajiya wayarki kar tayi lahani.

” Hamida wadda

tausayin Salma ya cikata, haka kawai taji ba

gaskiya ba ne abin da Hajiyar ta fada. Don haka ta

saci wayar Nafisa tayi cikin daki, ta kuma fada

bandaki.

Aliya ta kalli Hajiya “Kiyi hakuri bari in zuba

muku abincin.

** Ta ce,

“Saka wa Mamanku dai, ni

ai abincin nan ba zai ciwu ba sai an yi ta ta Kare a

yau din nan.

Nafisa ta ce, “Ai gara ayi, don ko da a ce kowa

ya yarda ni ba zan amince ba.

Son kai kiri-kiri. http://WWW.DAILYNOVELS.COM.NG

Aliya tace

“Ai ba yin kansa ba ne, ba ki ji abin da

Hajiya ta ce ba?”

Amna wadda ta yarda da zancen dari-bisa-dari

ta kalli Salma cikin tsana. “In dai tana gidan nan ni

kam ba zan zauna ba, don gaskiya bana son asirce-

asirce din nan.

Hamida ta kira sau uku kafin ya daga. Ya ce,

“Ya ya ne?”

Ta ce,

“Yaya don Allah ka zo gida

yanzun domin ga Salma din nan an tsare ta su

Hajiya.”

Gaban Shatima ya fadi, sam ya manta da tsanar

da Hajiya tayi ma Salma. Ya ce,

“Na gode

Hamida, gani nan zuwa.”

Lokacin tashi bai yi ba yaga cewa dole ne fa

yaje gidan don kashe waccan wutar da shaidan ya

rura a cikinsa. Ya dauki uzurin gaggawa ya fita.

Bai san irin gudun da ya yi ba, ya dai ganshi a

layinsu.

Yayi fakin lokacin ne Mustapha ya fito daga

falon Aliya, Shatima ya nufi gurinshi. “Ina su

Hajiyar?”

Mustapha ya ce,

“‘Suna falon Nafisa,

Ya Ce,

“To bari in je mu gaisa.

Mustapha ma ya

biyo shi don ya gama cin nashi abincin.

Tun daga Barandar yake jin muryoyinsu daya-

bayan-daya. Hajiya tana fadin

“Ba bakin dan

Akuya ba, ko da bakar Jaka ku ke asiri yau sai kin http://WWW.DAILYNOVELS.COM.NG

bar gidan nan

Amna cikin kuka tana fadin,

“Yanzun zan kira

Dad dina a zo a dauke ni, ina tsoron asiri.

” Nafisa

tana fadin “Jiyan nan sai da nayi mafarki da ita, ba

zan iya tuna me ya faru a cikin mafarkin ba, amma

tabbas na ganta.

Ni kaina in tana gidan nan Mama da ku zan bar

shi yau don ba za ku bar ni ba.

• Mustapha ne ya

fara shiga, hakan ya hana Aliya yin maganar da

taso yi, don ta hange shi tsaye.

Cikin tashin hankali ya shiga dakin inda gaba

daya suka maida kallonsu gare shi. Sannan

kowacce ta.shiga nanata abin da dama ya ji suna

fada.

Hajiyà ta ce,

“Duk kuyi shirunku, yanzun dai

ka zaba ko ni da na haife ka da iyalanka, ko

kuma wannan yarinyar ita kadai.

.” Ta nuno mishi

Salma wadda ke durkushe tana cikin firgici da

matsanancin tashin hankali.

Itama kallonshi take cikin tsananin bukatar

taimakonshi. Idanunta suna nuna shine kadai na

Karshe da ta ke sa rai zai yi wani abu a kan

wannan halin da take ciki.

Hajiya ta katse shi da fadin,

“Zan la’ance ka in

“ka sake kallonta. Kuma na baka minti daya rak!

Ka yanke hukunci.

Mu hadu a littafi na uku

HMMM LABARI FA NATA TAFIYA SHIN KOYA ZATACI GABA DA KAYAWA KUDAI KUCI GABA DA KASANCEWA DAMU A KODA YAUSHE WWW.DAILYNOVELS.COM.NG

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button

You cannot copy content of this page

Adblock Detected

YOU ARE USING ADBLOCK TURN IT OFF TO COUNTIUE BROWSING OUR WEBSITE