RANA DAYA BOOK 3 CHAPTER 25 BY HALIMA K/MASHI

RANA DAYA BOOK 3 CHAPTER 25 BY HALIMA K/MASHI

 

 


Yusuf yace gurin biki na ganta ranka ya dade a taimaka min

Shatima ya sake furzar da wani huci mai zafi sannan yace kanasin kace min kunyi hira da ita kuma ita ta kwatanta maka nan gidan ?

Yusuf yace magana daya kawai tayi min wai in barta wai tanada miji

Daidai lokacin salma ta turo kafar gidan sanye da kayan islamiya zata tafi turus ta tsaya tana kallon shatima da yusuf shatima cikin tsawa yace ke zonan jikin salma ya dau rawa tazo ta taugunna tace gani yaya

Ya nuna yusuf kinsan wannan?

Tace eh

Yace meke tsakaninku?

Babu komai don inma zai fadi gaskia aina fada masa inada miji

Shatima ya zabga mata harara yaya akayi yasan gidannan?

Hawaye suka soma zubowa daga idanunta tace ni bani na nuna musu ba yace to waya nina muku? Ya tambaya tare da kallon yusuf

Yace kawarta ce ta nuna min

Shatima ya kalli salma fada masa ko wanene mijin naki don ya sani

Salma ta dubi yusuf cike da jin haushinsa sannan ta nuna shatima wannan shine yayana kuma shine mijina

Shatima ya kalli yusuf to kaji kuma ina fatan ka gamsu sannan kuma ka fita hanyarta

Ya dubi salma ke kuma koma ciki ina zuwa

Cikin tsoron kar ya hana ta karatu; tace

-Wallahi ni.

Ya daka mata tsawa, “Na ce ki wuce ko?”

Salma ta nufi ciki. tare da fadin, “Na shiga

ukuna Ya bi bayan Salma ba tare da ya kara kallon gurin su Yusuf ba. Tana Kokarin bude dakinta da makulli ya iso kusa da ila, makullin ya fadi don tsoro. Gani take yi dukanta zai yi.

Yace Ke tsaya ki amsa min, kuma ki fada

min gaskiya Salma ta tsuguna jiki yana Bari, ya ce,Kina son yaron?”

Ta zaro ido da fadin,Haba Yaya, ina da

miji kuma zan so wani kamar jahila?”

Ta fada mishi duk yanda abin ya faru

Ta ce,Kuma Kawayena ba su san cewa ina

da miji ba Ya ce,

“To daga yau ina son duk Kawayenki

su san cewa ni mijinki ne, sannan daga yau kin gama saka mayafi sai hijabai”

Tace

*To ai banida hijabai, sai wanda aka

kawo kwanaki kasai mana

Ya ce. “To a kara kawowa in sai muku. Tashi

ki tafi islamiyya

Salma ta wuce tana gode wa Allah da ya tsare

ta.

Amna cikin motarta ta nufi gidan Maman

Afra, sun Kulle da Maman afra ne saboda yawan yin

siyayya da takeyi a shagonta, mijinta sojan samane

babban soja. Maman Afra jininsu ya hadu sosai da

Amna, don suna zuwa gidan juna tare da bai wa juna

shawara. Ta kofar kicin ta shiga bayan tayi fakin

Ta samu Maman Afra tana saka danwake, ta

ce A’a yau kuma ke da kanki a kicin?!”

Ta ce. “Ke dai bari duk na saka su aiki, ga shi

yunwa ta ishe ni, kuma danwake nake son ci”

Amna ta ce Dole ki ji yunwa sha biyu fa ta

gota Maman Afra tace, “Kin san mai house ya

dawo jiya da yamma yanzun na dawo daga kai shi filin jirgi ya wuce Lagos”

Amna ta zaro ido,

“Kwana daya rak?” Maman Afra tace

“Don ni kadai ya zo,

kuma na samar masa da nutsuwa ya tafi yana

kewata Suka sa dariya, tace

“Maman Jafar a wannan

zamanin mu fa ba a sanya, mata suna nan a waje birjik suna jiran wanda za su dafe mawa. Ke da mijinki kina kallo wata a waje tana mulkinsa.Domin

yanzu mata ba sa jira a taya su,

Ta dauki danwaken tana fadin, “Mu je ciki

Maman Jafar, game da miji bana sanya, ban hada shi

da kowa ba wallahi. Duk lokacin da ya z0 sai na bar masa wata alama wadda za ta sa in kasance a zuciyarsa kowane lokaci®

Amna ta isa ta dafa kafadarta, *Tsaya Maman

Afra, wace alama ce wannan? Ni fa dama matsala ce da ni

Ta dube ta, “Wace irin matsala ce? Kodayake

mu karasa dakina

Ta kwala wa ‘yar aikinta kira, “Haula!”

Yarinyar ta z0 da sauri, ta ce,

“Kawo min

fulas din shayi da dafaffen kwai*

Kan gado Amna ta haye, don tace ba ra ta ci

dan waken ba. Maman Afra ta zube kan kafet din Wai Maman Jafar wace matsala haka dake Amna tace

“Humm, mijinmu ne in muna

tare kowane lokaci a hira da lokacin sirri sai ya dinga kira min sunan kishiya. Ko fa magana zai min sai kiji ya ce Nafisa, sannan yace au Amna? Maman Afra

abin yana damuna wallahi’

Maman Afra ta zaro ido,

“To ke kuma ki ka ce me?

HMmm LABARI fa nata Tafiya shin KOYA ZATACI GABA da KAYAWA KUDAI KUCI GABA da kasancewa damu A koda Yaushe

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button

You cannot copy content of this page

Adblock Detected

YOU ARE USING ADBLOCK TURN IT OFF TO COUNTIUE BROWSING OUR WEBSITE