RANA DAYA BOOK 4 CHAPTER 18 BY HALIMA K/MASHI

RANA DAYA BOOK 4 CHAPTER 18 BY HALIMA K/MASHI

 

 

jikan jaririn nata. Da suka zo falo kuwa Shatima ya ce, “Kakata ina ta gaisuwa?”

Tayi banza dashi tana fadin,Maryama tashi mu je kin ji don ita ba ta bi su ciki ba, sai kuma taga ya kamata ta yi masa gori Daidai lokacin da ya ce,Kaka na san ni mai

laifi ne Ta ce, “Kai wa ka ke da suna ma? Karkaga na zo gidanku ka zata bikonka na zo, ni awa har da za ka gaida ni? Shi ke wulakanci a duniya  dama yi min ne in maka, yanda ka daki wata ka kora ta kai ma ga shi nan an kusan kashe taka yar uwar. In ka- ji zafin abin da akai wa Badi’atu to ka sani haka dan uwan Salma yaji. Sannan in uwarka da ubanka sun ji zafi, to su ma iyayen Salma sun ji. Bugu da Kari ga ta nan ita ma za ta soma zaman gida kamar Salma, ita ba bazawara ba ita ba me aure ba. Mu gani ko sai yaushe fim din zai kare!”Zancen Kaka ya doki Hajiya, Shatima

kuwa cikin sauri ya sha gaban keken Hajiya, ya durkusa yana fadin,Hajiya, ina son Salma

Ya kalli duk *yan dakin,Ku zama shaida

ina son Salma so mai tsanani, kuma matata ce” Salma ta kalle shi ta san wani sharadì

yake son cikawa nata. Ta tabe baki tare da girgiza kai alamun bai yi ba, ya ce,

“Ina sonki Salma Kaka ta ce,Mu je Salamatu kin ji wai saida ya ga an wa kanwarshi sannan ya san da yana sonki Ta karkata kujerar suka wuce ta gefenshi yana tsugunne. Ya mike ya bi su da kallo. Matanshi daga mai tsaki, sai mai kau da kai. Amna dai waya take dannawa ta yi kamar ba ta san ana yin wani abu ba.

Suna isa gurin mota Kaka ta rufe Salma da

fada tana cewa,Ke kuma da ma kyale ki na yi

duk waye-wayen da ku ke yi da shi ina jinku, nadai barki ne don na ga ba ki bada min kasa a ido ba. Saura da ya zo babu wani kamun kai da man martaba ki kwasa riba ki ba ki koma, ya kuma koro ki”Salma ta yi kus don ta ji kunya, ashe Kaka ta gane tana waya da Shatima?A daren ranar ba ta daga wayarshi ba, don haka ya turo mata sakon cewa, ya cika alkawari ya bayyana sonsa gare ta, kuma

a gaban wadanda ya bayyanar musu dakinta.

Ta ce,Aikinka bai yi ba, domin babu

kusan mutum uku a gurin. Ya yi lissafin su waye a wancan lokacin, kuma su waye yau? Sannan tace, ya yi hakuri ya daina kiran layinta. Hajiya ta zabga tagumi, ko ba a fada mata ba dole ta yarda cewa, duk abin da kayi ma dan wani sai an yi ma naka, hakan ya sa ta dauri aniyar cire bakinta daga kan harkokin cikin gidan Shatima, don haka ta samu Alhaji da kanta ta ce masa tana son ya shiga don Allah Salma ta koma dakinta. Ya ce,

“Yanzun da ki ka ga ke ma an yiwa

“‘yarki ko? To ni dai ba zan ce komai ba don

kuwa na shiga tun baya Kaka ta ce babu ruwana, kin ga dole ni ma in yi wa uwata biyayya ba zan yarda in saba mata ba. Don haka ke da ki ka hana shi zuwa sai ki tasa shi ku je Hajiya Amina ta ce,Ni ba zan iya zuwa

ba, don na jima ban je gidan Kaka ba”

Ya ce,Wannan kuma ruwanki Salma ta ki daga wayar Shatima, duk da irin sakwanni na magiya da yake turo mata tare da nuna son jin muryarta.Ranar juma karfe biyar na yamma Salma ce a kicin tana yi musu faten doya, Kamshinsa ya cika gidan. Shatima ya yi sallama tare da shiga falon. Kaka da ke zaune kan kujera ta amsa,amma tana ganin Shatima sai ta gimtse fuska. Ya zauna jiki a sanyaye ya sunkuyer da kai yana gaida ta. Sau daya tacE

“Lafiya Daga nan bata sake magana ba.

Maryama da ke shafa mata man zati

Kafa ta gaida shi, ya amsa yana son ya ce ina

Salma, yana tsoron kaka Salma ta fito daga kicin tana sanye da riga da siket na atamta.

A zamanta gidan Kaka ta koyi abubuwa masu yawa, cikinsu har da girki kowane kala. Da

yake yar aikin Hajiyar kwararriya ce gurin girki, sannan ta koyi tsafta duk da dama ita

din ba kazama ba ce. Hajiya Kaka ta ce.

“Ki sani zama da kwalliya a ka san

mace, ba wai mace ta zauna don tayi wanka ta saka kaya ki yi kwalliya sosai, kuma ki sa sabbin kaya ba wai sai in za ki fita ba”

Sannan ta koyi yin lalle, ta ce, mace ta

zama hannu da kafa fari tas? To me ya

bambantaki da namiji? In ba za kiyi irin namu

na da ba, to lallai ya kasance ki yi irin naku na

zamani. Wannan ya sa Salma ta kulla abota da falle da kitso. Haka kuma ta koyi zama cikin

kunshi. Tun kafin ta shiga falon ta ga takalman

Shatima a kotar daki, haka kuma Kamshin

turarensa ya cika gidan. Ta dubi jikinta ko da makusa? Sannan ta shiga falon.Kofa yake

fuskantowa, ya yi kyau cikin farin boyel tamkar

matashin saurayi,. Babu wanda zai kalle shiya

ce ya aje mace bare har da ya’ ya.

Salma ta yi saurin dauke kai daga kallon

Shatima ta dubi Hajiya Kaka. Ta tsare ta da

idanunta duk da suna cikin gilashinta mai kara

wa ido gani Salma yarinya ce mai hattara, zamanta à gidan Kaka ta gama sanin wace ce Kaka, domin ko kallo Kakar ta yi tana iya tantance abin da kallon yake nufi, don haka kai tsaye sai ta nufi cikin daki don ta fahimci Kaka tana kallonta ne ta ga Ina za ta? Kuma

wace karba za ta wa Shatima

Ganin ta shige daki sai Kaka ta maida kai

ga Maryama,Ba ni ruwan can in sha

Shatin’ wanda ya bi Salma da kallo har

sai da ta shige daki sannan ya kalli Kaka.

“Kaka don Allah kiyi hakuri, gani nazo

na kawo kaina Kaka Ta ce,

“Ni a wa? Da na isa ai tuntuni za kazo. Amma tunda sai da ishara ta sauka a gidanku

sannan kazo ai ba ni da ta cewa

Ka je in matarka taga ta iya Kaka babu ruwanta

Hmmm LABARI fa nata Tafiya shin KOYA ZATACI GABA da KAYAWA KUDAI KUCI GABA da kasancewa damu A koda Yaushe

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button

You cannot copy content of this page

Adblock Detected

YOU ARE USING ADBLOCK TURN IT OFF TO COUNTIUE BROWSING OUR WEBSITE