RANA DAYA BOOK 4 CHAPTER 25 BY HALIMA K/MASHI

RANA DAYA BOOK 4 CHAPTER 25 BY HALIMA K/MASHI

 

 

Salma cikin wasa ta ce,”Ya ya son

ranka?”Ya ce,Fari kar”. Suka sa dariya.

A ranar Salma da Shatima sun kwana

tare kuma cikin soyayyar ma’aurata, Shatima

ya yi alfahari da samun Salma budurwa, da ma

ya zaci haka. Salma ba ta yi wani raki ko nuna

wahalarta game da ranar ta farkonta ba, kuma

ta cire kunya don ganin ta sa shi farin ciki.

Washegari tamkar kada Shatima ya bar

dakin Salmar, jinshi yake wani sabon mutum a

yau. Ban da makarantar Salma da ta yaronshi

da ke yi can Abuja da gaskiya sai Salma ta

koma Abuja.’ Da zai tafi ya shiga dakin Salma tana shara, ya ce, Salma ta aje tsintsiyar hannunta ta rungume shi. Ta ce;Yayana za ka tafi?”Ya ce,Zan tafi Salmata,wallahi ina

sonki, zan yi kewarki”Ta dago ta dubi fuskarshi, hawaye ne a idanunta suna bin kimatunta.

Ya cika da mamaki Salma mene ne?”

Ta ce, Yaya yanzun bana son ka yi nisa

da ni” Ya sa hannu yana share mata tare da

fadin,Salma za ki sa in tafi cikin damuwa ki

daina hawaye”Ta yi murmushi,Bana son ka zauna da damuwa mijina, Allah ya tsare’Tamkar kada ya barta haka suka rabu cike da kewar juna.

Safwan koyaushe in dai yana gari, to

yana zirya gurin duba lafiyar Badi’atu, sai

hidima yake ta yi mata, kawo wannan kawo

wancan. Tun tana jin kunyarshi saboda kinshi

da ta yi, ga shi yanzun yana fama da hidimarta,

har dai ta dake ta daina jin nauyinsa. Ko da bai

mata maganar so ba tana sane har yanzun yana

sonta, kuma ya ga ba ta yi idda ba ne. sai dai

tana shirye duk randa ya furta kalmar so za ta

amsa masa.

Aliya dai kima ta riga ta zube, ko magana za ta fadawa Shatima sai ta dinga shakka, domin ta ga yanzun hira in ba abin da ya shafi shi da ita, ko kuma zancen danta, tana dauko wata maganar za ta ga ya yi mata shiru. Domin shi dai a gurinshi yanzun duk sun fi ta mutunci da kima.Ranar wata asabar Shatima yana kwance a gadonshi dakin Salma yana danna waya,Salma tana kicin tana

“yan girke-girkenta. Da* ta dora ta dawo ta kwanta a jikin Shatima ya sake mannota sosai, ya ce,Wai me ki ke dafa mana?’Ta ce,Ba ka ce ka jima ba ka ci tuwon semo ba?”Ya ce,Miyar me ki ke min?”Ta ce,Danyar kubewa”Wayarshi ta yi ruri, Amna ce. Ya daga da sauri don tun jiya ta ce masa ba ta jin dadì.Ta ce,Baban Jafar zazzabi fa ya rufe ni”Ya tashi da sauri,Bari in z0″Salma ta kalle shi cikin mamaki, ta rasa me ya sa kullum Shatima yake rawar jiki a kan Amna? Ya kalle ta tare da miko mata hannu,Zo mu je ki gaida ta

Babu musu ta mika hannu ya kama suka

tafi. Tana son sanin abin da amna ta ke masa

wanda yake sa shi maida kai cikin lamuranta.

Har cikin dakinta suka shiga tana kudundune a

kan gado cikin bargo. Shatima ya zauna tare da

bude sassan fuskarta ya sa hannu a dokin

wuyanta. Ta dan bude ido, Salma suka hada baki gurin yi mata sannu ita da Shatima, ya ce,

“‘Kin kuwa sha magani?”Ta ce, “A’a Salma ta ce,

“Ko dai a kai ta asibiti ne Yaya?”Ya ce, “Ina ganin zai fikawai”Amna ta ce,Ka ba nì parasitamal kila

ya sauka Ya ce Salma ta dauko, ya nuna mata

gurin aje magungunan. Ta ba shi, sannan ta

nufi firji don ba ta ruwa. A nan ne ta ga gororin

tsumi a wani dan lungu, ga gumba. Salma ta yi

dan murmushi, da ma ta zargi haka, tana gani a

cikin littattafai Shatima ya ba ta da kanshi ta sha,

sannan ta kwanta. Ba su bar dakin ba sai da

bacci ya kwashe ta.

Salma yarinya ce mai dabara, sannan ta

samu Karin basira a cikin karance-karancenta,

sannan cudanya da wayayyun yan boko ya sa

ta zama wayayya, ga girke-girke da ta kware

na gargajiya gidan Kaka, na zamani kuma a

karance-karancenta.- Sannan kuma ‘ tana

fahimtar abin da mijinta ke so da wanda ba ya

so. Sabuwar rayuwa ta bude a gidan na Shatima, cikin dabara za ta shige mama duk

wani daya danganci Shatima tun daga

matanshi,ya’ yanshi zuwa danginshi.

Azumi ya kama ga makaranta, sai dai cikin

goman faro aka tafi yajin aiki duk daukacin

jami’o’in garin nan, ko in ce kasar sai

daidaiku. Wanna ba sabuwar matsala ba ce a

Kasar nan domin zai wahala ka soma karatu

jami’a ka kare shi lau ba tare da ka ci karo da

matsalar yajin aiki mai bata lokaci ba.

Salma ta lura sosai Shatima yana da

matsala da matanshi biyun nan na cikin gidan

Amna da kuma Aliya kwarai ta sha mamakin

na Aliyan, amma ta san abu ne mawuyaci ta ji

daga bakinshi. Inda ta gane na Aliya in ya zo

ya sauka dakinta wanka yake ya fice, kuma in

ya koma washegari zai sake ficewa, in ya

kwana gurin Amna ba ya fita har lokacin

tafiyarshi sannan ya wuce. To in ya sake zuwa

ita kuma dakinta zai sauka, kuma ba ya fita,

haka washegari har sai in ya koma dakin. To

kuma ita ma Amna din yanzun sai Salma ta

– lura in yana dakinta ba ya zama. Lallai akwai

dai wani abu, tsoronta kar dai Shatima ya canza

hali yana yawo.

Hmmm LABARI fa nata Tafiya shin KOYA ZATACI GABA da KAYAWA KUDAI KUCI GABA da kasancewa damu A koda Yaushe

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button

You cannot copy content of this page

Adblock Detected

YOU ARE USING ADBLOCK TURN IT OFF TO COUNTIUE BROWSING OUR WEBSITE