RANA DAYA BOOK 4 CHAPTER 26 BY HALIMA K/MASHI

RANA DAYA BOOK 4 CHAPTER 26 BY HALIMA K/MASHI

 

 

Da safe bayan sun yi sallah da karatun

‘al kur”ani sun koma sun kwanta, sai Salma ta ji

wayar Shatima tana ruri. Ba ta motsa ba don ta

san shi ma yana ji. Yana dagawa sai ta fiji yana

•gaisuwa cikin girmamawa, ta ce a ranta, kamar

Alhajinsa? Sai kuma ya tashi daga gadon ya

tafi daf da fita yana fadin,Daddy ba haka ba

ne. ban san Amna da karya ba sai dai in yanzun

za ta fara tunda idonta ya rufe tana son ta cutar

da ni. Wancan karon kun sa baki Daddy a kan

maganar tsarin iyali na hakura don bana yin

jayayya da iyayena, tana ta tsarinta don ni dai

naira ban bayar ba, kuma ba ni da niyyar

bayarwa. Allah ya nuna mata ikonshi duk da

tsarin ya ba ta ciki sai ta ce sai ta zubar da shi?

In ba ta tsoron lafiyarta ni ina son cikina, kuma

wallahi Daddy a fada mata gaskiya komai zai

iya faruwa inta cire man ciki?? Daddy yace

“Kai saurara ka ji! Shi fa ciki yarjejeniya ne na mutum biyu, don kai ka yarda ita ba ta amince ba kenan babu dole ta barshi, musamman da yake ita ce za ta yi kayan daukarshi a jikinta. Sannan kana ta fadin cewa,in ta cire komai zai iya faruwa, ka san dai ba zaka iya shara’a dà ita ba, karkari dai ka ce ka sake ta, kuma ta fada min ita ta shirya ma haka.Ni na kira ka ne in ba ka shawara ba wai rokonka zan yi ko hana ka daukan duk matakin da ka so ba, a’a shawara ta ka lallaba, ka lallashi matarka in ta ki ku je a cire, ba kana da

wasu yaran ba? Kuma sauran matanka za su ci

gaba da haihuwa, wannan shine kawai

Shatima ya ce,Gaskiya dai ni wannan

shawarar ba duka zan dauka ba, don ba zan

bari fa ta cire min ciki ba wallahi, kuma babu

saki a tsarina amma zan bi hakkina

Daddy ya ce,Shi kenan, tunda ka ki ka

iya yin duk yadda ka so Sai ya kashe wayar.

Shatima ya ja dogon tsaki yana fadin,

“Za a yi haka da mana sani. kullum suna bayan

‘yarsu don son rai ga gaskiya kiri-kiri.

To ni ba zan zama sakarai ba Yana kwanciya

tare • da wani tsakin,Salma ta kai hannu ta kamo shi zuwa jikinta,

“Don Allah ka yi hakuri Yaya. Duk da ni

yarinya ce bai kamata in saka bakina cikin

zancen manya ba, don na fahimci komai daga

zantukanku, ko in ce daga amsarka. Ka lallaba

ka bi ta a hankali, kuma ka sa hikima”. Ya ce,

«Wace hikimar zan saka mata ga gaskiya ana kallo?”Salma ta ce,To yanzun in ka bi ta ta

kuna ta fada da gaba, cikin wanna rikicin ma

sai ta je ta cire ba ma ka gari. Amma in ka

lallabata ka nuna mata kamar ka yarda, sai ta

saki jiki har ma ka nemi shawarar ina take ga

za a cire, in ta fada kai kuma sai ka yi maza ka

samu gurin da asibiti ke ko likita mai zaman

kanshi, ko dai ina ne a nan in ka je kana da

zabi biyu. Ko dai ka ce masa in kun zo ya yi

mata dabara ya ba ta abin da ba zai zubda ciki

ba, gaba baya sai ya nuna mata in ta nace sai ta

zubar zata rasa ranta.Na tabbata dole ta

hakura, ko kuma ka gargadì shi wanda za ku je

din kafin ku je, kan cewa hukuma za ta raba ku

matsawar ya yarda ya cire mata ciki. Kuma

dabarar zuwa gurin wanda ta sani shine, don

za ta fi yarda da wanda ta ke son ya yi mata

aikin fiye da wanda kai ka ke so. Sannan in ka

kai ta gurin wanda ka ke so za ta iya komawa

gurin wanda ta ke so, sai dai fa Yaya ka yi

hakuri.shawara ce ba dole sai ka dauka ba,

kwakwalwarmu ce ta yara sai ka yi watsin da

zancena Cike da al’ajabi ya dube ta, har zai yaba

mata, sai kuma ya tuna da Aliya da irin sigar da

ta zo masa kenan amma da ya saki jiki karshe

sai ta ba shi mamaki. Ya aje numfashi, ba zai ci

gaba da yin shawara da wata game da matsalar

wata ba, abin da kawai zai yi shine, kowacce

zai tafi da ita a kan matsalarta, YaCE,

«Salma ba lallai in dauki shawarwarinki ba duk da cewa kin yi basira”.Ta Ce,Da ma ban ce sai lallai ka yi amfani da ita ba, da ka saurare ni mana gode Duk shawarwarin da Salma ta bada su ya

bi, kuma cikin sati hudu ya cimma nasara,

Amna ya hakura bisa gargadì da tsoratarwar

likita,wanda ya samu suka tattauna bayan

Amna ta fada masa cewa gurinshi za ta je. Har

ma ya tambaye ta yanda aka yi ta sanshi, ta ce,

shine ya saka mata abin tsarin iyali, kuma ta

sanshi ne ta hanyar kawarta Maman Afra

wadda ta ki yarda da shawarta a wannan karon.

Har ma sun dan yi yar sa’insa sakamakon ta ki

bai wa Amna goyon bayan cire cikin.Shatima

ya ji dadin yanda shirin na Salma yayi

kai tsaye bai samu kowace tangarda ba. wata juma’a gurin Salma zai  diro, da wuri ya taho jirgin sama ya biyo don cike yake da kewarta, wancan zuwan da ya yi bai samu kwananta ba duk da kwana biyu yake yi. •Da ma wani satin da

ya gabata kafin wannan ya samu ba ta sallah. Ta zuba kitso shuku Kanana, ga lallenta hannu da kafa an watsa mata tamkar amarya,kayan turawa ta saka riga da wando, wandon siriri bai kai kasa

ba, rigar kuwa kadan tafi gwiwa.Tunda

Shatima ya shigo da runguma ta tare shi, haka

kuma kai kawon shirya masa abinci da take yi,

shi’awa take ba shi ga mayen Kamshinta da ya

nace a dakin.Waina ta yi masa da miyar tantakwashi, ga lemon zo6o mai sanyi ya ji kokonba. Tare suka ci abincin cikin wasannin bai wa juna tare da hirarrakin miji da mata masu fahimtar juna.Wayar Shatima ta shiga ruri, Nafisa ce ta kira shi don jin ko ya sauka lafiya? Wannan

halin yana cikin halayen Nafisa wanda Shatima

ke so, wato nuna kula da tafiyarsa in ba ya tare

da su. Lura da hakan ya sa Salma kwaikwayon

Nafisar domin ita ma ta kara samun mazauni a

zuciyarsa,Shatima ya daga wayar cikin jin dadì yana fadin, ‘Matata

Hmmm LABARI fa nata Tafiya shin KOYA ZATACI GABA da KAYAWA KUDAI KUCI GABA da kasancewa damu A koda Yaushe

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button

You cannot copy content of this page

Adblock Detected

YOU ARE USING ADBLOCK TURN IT OFF TO COUNTIUE BROWSING OUR WEBSITE