SALON SO CHAPTER 9

SALON SO CHAPTER 9

 
 

Faruk ya ce, “Ba ruwana babu inda za ni bare ta

zo ka ci mata mutunci ta zo ta rinka ganin h rashin

kirkina.

Haidar ya ce, “To ni ka kai ni wajen ta na ganta,

Faruk ya yi murmushi, Haidar ko dai ka so ma

son ta ne?”

Haidar ya rintse ido ya ce, “Wallahi ban san

lokacin da son yarinyar nan ya yi min dirar mikiya

ba, ya shige ni.

Inna kwanta da daddare Allah Allah nake gari ya

waye don na ga kyakkyawar fuskar matata kuma

kanwata, wallahi ni kadai na san yanda tsananin

son jawahir yake raina, kai abin da na yi wa

Kausar a gananta ma na yi ne don na auna na ga

tana so na kuwa ko ni kadai nake shirme na.

Faruk ya ce, Ka ga irin abin da na so ka gane

tuntuni ka ki, to yanzu kuwa in ta ji halin da kake

ciki sai ta ce don ka ga ba za iya kwanciya da ita

ba ne, shi yasa ka nemi shiri da ita.

Haidar ya ce, “Ai likita ya ce zan warke fa”. Ko da

yake yanzu ne lokacin tantance wanda take

sonka don Allah da wadda a kayi auren sha awa.

“Haidar ya ce, Ni dai don Allah ka je ka taho min

da sahibata ko don na ga halin da take ciki.

Faruk ya ce, “Zan je ai yanxu

Kausar ta turo kofar ta shiga fuskarta a murtuke

babu alamar fara’a, ta je gefe daya ta zauna ba

tare da ta kula wani a cikinsu ba. Faruk ya mike

Haidar bari na je in dawo ko? Duk yanda muka yi

zan zo ka ji.

Ya ce, “Don Allah ka je fa yanzu kada ka ki zuwa

ka ji. Faruk ya ce Insha Allahu kuwa yanzu zan

je.

Faruk ya fita ya bar su Haidar ya juya ya kalli

Kausar ya ce, “Me ya same ki ne na ga kamar

ranki a ba ce? Ko cikinne yake ciwo?”

Ta zumbura baki, “Kai yanzu har ka manta da

barnar da Jawahir ta yi maka a jikinka har kake

cewa a je a taho da ita? To wallahi ni ba zan

yarda ba don ta ga ita ba ta da amfani a wajenka

shine za ta nakasta min kai, wato ka zamo marar

amfani, to wallahi ba zan yarda ba don ita ma sai

na nakasta ta, sai dai duk abin da za a yi a yi.”

Haidar ya daka mata tsawa ya ce, “Ke ki shiga

hankalinki kina ganin duk da son da nake wa

jawahir da ta yi miki abu sai da na yi mata marin

da ta gigice, to wallahi ki shiga hankalinki idan

kika sake kika taba min mata wallahi sai kin yi

mugun raina kanki, don sai kin yi mamakin abin

da zan yi miki.” Ta mike ta yi waje tana kunkuni

ta zari mota ta nufi gidan Yakumbon Haidar wato

kakarsa ta wajen uba, ta je ta zayyane mata

maganganun karya da gaskiya ta gaya mata,

Yakumbo ta hau sababi ka ji mu da tsinanniyar

yarinya don ba ta son sa shine take neman

hanyar kashe shi, to wallahi bi ba yarda zan yi

ba, tashi ki koma asibitin gani nan zuwa yanzun

nan, “Kausar ta koma asibiti ta tarar su Anti da

Momy da su Yaya Abba sun cika asibitin taf, ana

ta jajen abin da ya faru.

Shi kuwa Faruk da ya je gidan Haidar yayi

sallama falon, su jawahir suna daga kicin suka

amsa sallamar suka fito falon, Faruk ya nemi

waje ya zauna jawahir da Bilkisu suka gaishe shi,

faruk ya ce, Haidar ne ya turo ni na zo na ga

halin da kike ciki in kuma da hali ki zo mu je yana

son ganinki. “Jawahir ta sunkuyar da kai ta ce,

“Gaskiya Yaya Faruk ba zan je inda yaya yake ba,

don in na je ban san irin wulakancin da zai yi min

ba, ka ga kuwa da na je ya bata min rai ai gwara

ban je ba.

Faruk ya ce, “Wallahi Haidar yana wani hali na

mutuwar sonki kin san miskilancinsa ya rasa ta

hanyar da zai bi ya nuna miki Kaunar da yake

miki don yanzu da kin ga irin magiyar da lallamin

da ya rinka yi min sai na zo gare ki dakin

tausaya masa.

Kafin ta yi magana Bilki ta ce, “Faruk bari mu

karasa girkin da za mu kai masa sai mu fito mu

je.” Faruk ya ce, to shi kenan bari na je na dawo.

Bilki ta zuzzuba komai a fulas ita kuma jawahir

ta je ta shiga wanka ta fito ta shirya cikin atamfa

ja! Super Holland dinkin filet ne ya kama jikinta

sai zani da dankwali da ta daura, farar hoda

kawai ta shafa a fuskarta sai dan man leben da

ta shafa ta dauko jan mayafi da jan takalmi ta

saka, kunnanta fashon din yari ne me jan dutse a

tsakiya. Bilkisu ta tafa mata “Amma

yarinyar nan kin yi kyau, kwalliyar taki ta burge ni

sai dai kash kin manta a shafa hadin turarukanki.

Jawahir ta yamutsa fuska, “Kin san fa inda za mu

je za ki ce na shafa hadin turare. Bilki ta ce, to

meye ba wajen mijinki za ki ba, ai gwanda ki

shafa turarukan da kamshinsu zai gigitar da shi

kuma ga karin lada a wajen Ubangiji, don duk

sanda mace ta yi abun da zai farantawa mijinta

har ya ji dadi a ransa to Ubangiji zai ba ta ladan

da ba ta san adadin yawansa ba.

Jawahir ta ce, Haka ne bari na shafa don na

fuskace shi yana son kamshi.

Sun jejjera fulas-fulas din a dan kwando me kyau

ta lullube shi da farin yanki me adon bakin les da

fulawoyi a jiki. Faruk ya dawo suka dunguma a

motarsa zuwa asibiti.

A lokacin ba kowa duk sun tafi sai kausar kawai

da take zaune kan kujera tana karanta jarida, ba

ta daga kai ba balle ta kalli wani a cikinsu. Faruk

ya ce, “To ga ta nan na cika alkawari ko, ga ta

na kawo maka

Haidar ya yi murmushi ya ce, “Ai kuwa na gode

Bilkisu ce ta fara gaishe shi tare da yi masa ya

jiki. Cikin fara’a ya ce, “Ai jiki Alhamdullahi.”

Jawahir ta durkusa cikin dari-dari da rawar

murya Kamar

mai shirin kuka ta ce, “Yaya ina wuni? Ya jikin?

Ya ce, “Lafiya lau jawahir ya naki jikin.?

Ya sa hannu ya dago ta daga tsugunnun ya shafi

kuncinta, ya ce, “Wai haka kuncinki ya tashi

hannuna ya fito radau na marin da na yi miki,

sorry Babyna ki gafarce ni, “Kafin tayi magana

aka turo kofar aka shigo tare da sallama,

Yakwalkwal ce ta shigo rike da hannun Sayyid.

Sayyid ya fincike da gudu ya nufi jawahir yana

cewa, “Anti na anti na, shine rannan kika gudu

unguwa kika bar ni ina ta kiran ki ba ki zo kin tafi

da ni ba. “Jawahir ta dauke shi ai yau da kai zan

tafi kai ta kwana a can ko? Jawahir ba ta ankara

ba ta ji saukar mari a kuncinta, Yagwalgwal ce ta

kuma hau fada, “Annamimiya me kuma ya kawo

ki wajen jikana kin so ki kashe shi, Allah bai baki

nasara ba shi ne kika biyo shi nan ki karasa shi

ko?

Haidar kuwa tuni ya diro daga gadon jinyar ya

tare jawahir yana cewa, “Haba Yagwalgwal ya za

ki doke ta ita ma fa ba lafiya ce da ita ba, me ta

yi miki?”

Yagwalgwal ta ce, “Ubanka ta yi min, shege

sallamamme so kake yanda uwarka ta mallake

Alhaji kai ma jikan mallake ka za ayi,

“Yagwalgwal ta ci gaba da nuna jawahir da dan

yatsa tana yi mata sababi, daga yau na gaya miki

ba ke ba Haidar in ke mayya ce ki ci kanki da

kanki, haka kawai hankalinsa ya kwanta yana

zaune da matarsa lafiya za ki zo ki bata musu

zama.

Jawahir ta mike jikinta ba kwari za ta fita Haidar

ya yi saurin riko hannunta yana cewa, “Haba

Yagwalgwal ya za ki zo ki korar min matata ki ce

sai ta tafi? Ai ba ita ta kawo kanta ba ni na sa a

je a dauko ta in ta tafi waye zai yi jiyya ta?

Kawai mutum da matarsa a nemi raba su. Kan ya

rufe baki bakinsa Yagwalgwal ta ba shi nasa

marin ya dafe kunci ita kuma ta ci gaba da

sababi tana nuna shi da dan yatsa, “Ka shiga

hankalinka ka san da wacce kake magana, idan

ba ka san ciwon kanka ba ai ni na san ciwonka,

yarinya ta nakasa ka ka zamo marar amfani

amma ba za ka guje ta ba, wata rana ma ranka

za ta raba ka da shi.

Jawahir ta fincike hannunta ta yi waje cikin sauri

Haidar ya yunkura zai bi ta Yagwalgwal ta rike

shi, Bilkisu ta bi bayan jawahir yayin da Faruk ya

rufa musu baya. Da kyar da ban hakuri ya shawo

kan jawahir ta shiga motarsa don ya mayar da su

gida. Faruk ya ce, “Don Allah don Annabi jawahir

ki yi hakuri da abin da tsuhowar nan ta yi miki.

Jawahir ta yi saurin katse shi, “Haba yaya Faruk

ka fi kowa sanin ta yanda a ka yi aurenmu da

yaya, ba son sa nake yi ba na aure shi don

biyayyar iyayena na zo nake zaman hakuri da shi,

ya tashi ya dankaro min kishiya ni duk hakurin da

na yi a kansa ba a gani ba kenan.

Fashe da kuka Faruk ya ci gaba da rarrashinta ki

yi hakuri jawahir ki tuna aure kike, aure kuwa

bautar Ubangiji ne kada bacin ran wasu ya sa ki

sabawa megidanki kin ji?”

Yanda na san ki da hakuri da ladabi da biyayya ki

ci gaba da yi komai me wucewa ne wata rana sai

labari kin ji?”.

Ta daga kai ya ce, “Yauwa ko ke fa gobe ku

shirya da wuri sai na zo na kai ku ta ce to. Ya

sauke su a gidan shi kuma ya koma asibitin shi

kuwa Haidar tun bayan fitarsu jawahir da

Yagwalgwal ta rike shi don kar ya bi su gado ya

koma ya kwanta ya yi rigingine ya rufe idonsa.

Maganar duniya babu wadda ba a yi masa ba

amma ya yi musu shiru ko motsi bai yi ba dole

suka gaji suka hakura suka bar masa dakin.

Faruk ya shigo ya dinga lallaminsa yana ba shi

baki tare da va shi hakuri sannan ya tashi ya

jawo kwandon da jawahir ta jero masa kayan

abinci.

Dakakkiyar sakwara ce lukui da miyar agushi mai

wadataccen nama, sai jalof din taliya da lemon

kwakwa. Haidar ya ce, “Ka ga yarinyar nan da

zan bata mata rai ba za ta ki yin abinci ba don

gudun kada ta bar ni da yunwa.” Faruk ya ce, ai

haka ake so ka ga yanzu sai ka rike ta da kyau

ka nuna mata garanci wanda ba ta samu ba a

baya. Haidar ya ce, “Allah dai ya ba ni lafiya amin

in ji Faruk yayin da ya zuba musu abincin a filet

din da ta zubo suka ci sosai dan shi kansa Faruk

ya yaba da dadin girkin nata.

Can kuwa Bilki ta mike don tafiya gida, “To ni zan

tafi jawahir sai dai gobe zan zo da wuri na raka

ki mu sake dubo shi. Jawahir ta hangame baki ta

ce, “Don kin ji Faruk ya fada ba kya tsoron mu je

a yi mana wani sabon wulakancin da ya fi na

yau.?

Bilkisu ta ce, “Insha Allahu hakan ba za ta faru

ba gwanda ki je, kada su samu kafar raba ki da

mijinki ga shi kuma yanzu kuna son juna. Jawahir

ta ce, “Shi kenan Allah ya kai mu goben na gode

Bilki da kaunar da kike min, da ba ni shawarwari

masu kyau da kike yi, Allah ya kara mana dankon

zumunci a tsakaninmu amin. Da haka suka yi

sallama ta tafi.

Jawahir ta shiga dakinta ta kwanta tana tunanin

abin da ya faru yau da ita.

Faruk ya fita ya yi sallar insha Haidar ya kalli

Kausar ya ce ke ba za ki yi sallar ba ne na ga ko

magariba ba kiyiba?

Ta ce, “A’a ina ruwanka a yin sallah ta ka ga

malam kawai ka ji da abin da ya dame ka. Faruk

ya turo kofar ya shigo Kausar ta zuba masa

harara tare da jan tsaki ta mike ta bar dakin.

Faruk ya taimakawa Haidar ya yi Sallah, Haidar

ya daga hannu sama ya dade yana addu’a

sannan ya shafa ya xuba tagumi.

Faruk ya cire hannun tagumin ya ce, “Haba

malam menene kuma? Ka yi hakuri a kan larurae

da ta same ka, ka yarda da kaddara ko?

Haidar ya ce, wallahi ba wannan ne ya dame ni

ba halin da jawahir rake ciki nake tunani kada fa

ta Gudu

gidan Inna ta kuma boye ta ka san ranta ya ba ci

dazu da abin da Yagwalgwal ta yi mata. Faruk ya

ce, “Ba na jin za ta fita har gida na kai ta kuma

na babbata hakuri ka san yarinyar akwai biyayya”

To don Allah ka je ka taho min da ita ta kwana a

wajena ka ga gidan ba kowa sai masu aiki.

“Faruk ya ce, “Ka yi hakuri da safe ai za ta zo ka

ga yanzu dare ya yi yanxu haka ma ta kwanta.

Haidar ya ce, “Haba Faruk don Allah ka taimaka

min ka je ka taho min da jawahir yanzu duk

girman gidan nan ta kwana ita kadai sai masu

aiki? Faruk ya ce, “Shikenan bari na je amma sai

na biya na dau Hafsa don ita ma ta zo ganin

likita.”

Haidar ya ce, “Ko dai ta harbu ne.? Faruk ya yi

murmushi ya ce, “To ga mu dai ga Allah don mun

sa rai.

Ya fita yana dariya ya biya ya dauki matarsa

Hafsa suka tafi. Ya ce, Ya ku ka yi da likitan? Ta

ce, “Gwaje gwaje ya yi min ya kuma dauki

fitsarina ya ce da safe a zo a karbi result din.

Faruk ya ce, “To Allah ya taimaka mana ya sa

abin da muke nema ne, ta ce Amin. Suka yi wa

juna murmushi.

Suka yi fakin a harabar gidan Hafsa ce a gaba

don ita take buga kofar falon nasu da yake kulle.

Jawahir da take takure a falo don zuciyarta cike

take da tsoro da fargaba ka sancewar ta ita kadai

a sashen ta yi tunanin ko ta kirawo ‘yan aikin

Kausar su taya ta kwana sai kuma ta fasa, to jin

bugun sai ya dada tsoratar

da ita. A tsorace ta je gaban kofar cikin rawar

murya ta ce, “Wanene?” Faruk ya ce, “Bude mu

ne, ta kalli agogo karfe tara gabanta ya fadi,

Allah ya sa dai lafiya? Ta bude kofar ta ba su

hanya suka shigo Faruk ya ce, “Sarkin tsoro da

kin zata barayi ne suka zo sa ce ki?” Ta yi dariya

ta kamo hannun Hafsa ta ce, “Wai yaushe rabon

ki da gidan nan? Ko da yake ban sani ba ko kina

zuwa wajen amaryarku Kausar, “Hafsa ta yi

dariya ta ce, Ni ina zan zo gidan nan mutuniyata

ba ta nan ta gudu ta bar min abokin miji ya zamo

abin tausayi a gari?” Ga ba daya suka yi dariya.

Faruk ya ce, “Kar dai a gaji da mu dan mun kuma

zuwa da kokon bararmu da karin ban hakuri

megida ya ce, a zo a tafi dake don Allah ki kwana

a wajensa. Ta yi shiru can ta ce gaskiya ni ba

zan je wajensa na kwana ba. Faruk ya ce,

“Subhanallahi, kin san hukuncin matar da mijinta

ya yi kiranta ta ki zuwa kuwa? Ko kina so ki

hadu da fushin ubangiji ne?

Jawahir ta ce, “Gaskiya Yaya faruk ba zan je ba,

ba Kausar tana can ba?

Ai ita ta saba kwanciya da shi ni in na je ina da

abin da zan yi masa ne? Faruk ya ce, “Haba

jawahir kada ki yi haka mana da iliminki da komai

ki yi hakuri ki amsa kiran mijinki mana.

Ta ce, “Haba yaya Faruk har ka manta irin

zaman da na yi da yaya Haidar a gidan nan ni

bani da hakki a kansa sai shi yanzu yake da

hakki a kaina har zai neme ni?” Ta sa kuka ta

mike tayi daki, “Wallahi ba inda zan je”. Ta turo

kofar dakinta ta kulle.

Hafsa ta ce, “Gaskiya fa ni fa ban ga laifin jawahir

ba, don gaskiya an zalinceta” Faruk ya dakawa

Hafsa tsawa tare da cewa, “Yi min shiru ana

neman sasanta magana kina dada tunzurata. Ya

jawo wayarsa ya yi danne-danne. Haidar ya

dauka, “Hello” Yauwa Haidar ka kwantar da

hankalinka kayi hakuri mun zo mun tarar jawahir

tayi bacci amma don Allah kada ka tsayar da

hankalinka da safe kafin na tafi office zan biya na

dauko maka ita. Haidar kafin ya ce, wani abu tuni

Faruk ya katse wayar ya kuma kasheta gaba

daya don ya san halin Haidar ba kyale shi zai yi

ba.

Haidar kuwa tun daga lokacin wata zuffa ta rinka

tsiyayo masa, hankalinsa ya yi mummunan tashi,

jikinsa sai rawar sanyi yake yi. Ba jimawa zazzabi

mai zafi ya rufe shi. Nan da nan jiki ya rikice a

ranar da sai Abbansa ne da yaya Abba suka

kwana a wajensa. Ba shi da wata magana sai ta

ambaton an bar jawahir ita kadai a gidan nan sai

masu aiki kada wani abu ya samar masa ita.

Yaya Abba ne yake dan karfafa masa gwiwa yana

tunasarsa. Yawan ambaton jawahir da Haidar

yake yi ya sa Kausar ta yi fushi ta baro asibitin

ta dawo gida. Jiyya ta koma hannun yaya Abba

da Faruk, amma asibitin kullum cike yake da yan

uwa da abokan arziki sai dai rashin matansa a

wajen. Duk da haka Yagwalgwal ba ta fasa yada

habaici da kananan maganganu ba don haka Anti

ba ta son yawan zuwa don ita take yiwa

habaicin.

Kamar ita ta haifa mata Haidar din

Yau kwanan Haidar hudu kenan a asibiti suna zaune a

dakin jinyar, Faruk da yaya Abba Haidar ya ce da

su, Faruk da yaya Abba ku fara hada kaya ku

karbo min takardar sallama.” Yaya Abba ya ce,

Ah sabo da me? Cikin raunanniyar murya Haidar

ya ce, “To kun ki zuwa ku rarraso min jawahir ta

zo gareni na ganta ko hankalina ya kwanta. Tun

da haka ne gwanda na koma gidan na yi jinyata a

can inda zan samu kulawarta.

Shi dai yaya Abba ba ya son jawahir ta zo wajen

nan ko don sabo da kananan maganganun da

Yagwalgwal take yi, don haka ya yi shiru bai ce

komai ba. Haidar kawai ya fara hada kaya Faruk

ya tausaya masa, ya ce, “Bari Haidar yi hakuri

bari na je yanzu na shawo kanta insha Allahu za

ta zo.

Jawahir tana zaune tana bitar karatun Alkur’ani

wayarta ta yi kara. Ta tsagaita da karatun ta

dauka, “Hello wa ke magana? Faruk ya ce, “Ni ne

daman na bugo na gaya miki Haidar yana cikin

dayan biyu ko mutuwa ko rayuwa, don ya rikice

an rasa gane kansa sai kiran sunanki kawai yake

yi”

Jawahir ta gigice, “Na shiga uku yaya faruk

yanzu ina yayan yake?

“Yana can asibiti a rikice.”

“Wayyo yaya faruk! Don Allah ka kwantar masa

da hankali yanzu zan zo.” Ya ce, “Ina harabar

gidanku ina jiranki ki fito da hanzari.

Kafin ya rufe bakinsa ya ganta ta fito da wayar

kange a kunnenta. Ya bude mata bayan motar ta

fada, shi kuma ya shiga gaba ya tuka suka yi

gaba. Yana tsayar da motar jawahir ta bude ta

fito a guje ta shiga dakin da yake tana danna kai

ta tarar da shi a gado yana ta faman ihu.

“Wayyo Allah! Ya dafe cikinsa yana ta juyi.” Ga

shi dakin sai shi kadai ba kowa, nan da nan

hankalin jawahir ya tashi, tausayinsa ya kama ta

sai kawai hawaye taji yana zubowa daga

idannuwanta ta zauna a gefen gadon ta dago

kansa ta dora a cinyarta tana rike da shi sai

sannan take yi masa, gani take da tana da ikon

cire ciwon nan ta dawo da shi jikinta da ta yi

domin kawai ya huta a abin da yake damunsa.

“Sannu yaya na kirawo likita ya ba ka magani.

Wayyo yaya cikinka ne yake ciwo? Yaya ko ina

ciwon yake yi?

Sannu yaya, bari na hada maka tea ka sha ko?

Ko za ka iya cin abincin? Don Allah yaya ka

tashi.

A hankali nishi ya lafa sai kadan kadan daga can

ya yi shiru ciwon ya tafi kenan. Jawahir ta

rankwafa kansa, “Sannu yaya”. Ya lalubi

hannunta ya danke a nasa cikin magana sanyi-

sanyi irin wanda yake jin jiki ya ce, “Yaushe kika

zo? Ta ce, “Ban dade da zuwa ba. Ina yaya

Abban ya tafi ya barka kai kadai?”

“Yanzu nan kafin ciwon ya tashi ya tafi gida

amma yanzu zai dawo.”Ta ce “Amma dai bai

kamata su rinka barin ka kai kadai ba kana cikin

wannan hali.”

“To ya zan yi jawahir ke ma da kike ‘yar uwata

matata kin guje ni kin ki jiyyata waye zai jura?”

Jawahir ta ce, “Ka yi hakuri yaya ba wai na ki

zama a wajenka bane ka san halin Yagwalgwal

kar ta zo tana tsinka na a asibiti shi ya sa.

Haidar ya ce, “To shi kenan ba komai zan nemi

likita ya ba ni sallama sai mu koma gida na yi

jinyar a can ko?”

Ta ce, “Haba yaya gwanda ka zauna a nan din ka

ga sun fi kulawa.”

To jawahir ai ba zan juri rashin ganinki ba

gwanda dai na koma gidan.”

Daidai nan likita ya shigo ya dubi Haidar ya ce,

yanxu ina ganin za mu sallameka ka koma gida

tun da Abbanka ya ce kasar waje zai futa da kai.

Don haka ga takardar sallama.

Jawahir ta ce, “To likita yawan ciwon cikin da

yake fa? Likitan ya ce ba komai wannan mun

bashi magunguna sai dai a dinga kula wajen ba

shi ya sha.”

Anan yaya Abba ya shigo ya kalli jawahir ya ce

wato sai yau kika ga damar xuwa wajen mijinki

ko? Kina sane da ba shi da lafiya yana kwance a

asibiti amma ba za ki zauna kusa da shi ba, don

taimaka ma sa ba ko.?

Jawahir cikin biyayya jawahir ta ce, “Kayi hakuri

yaya insha Allahu ba zan sake ba, “Faruk ya

shigo suka kwashi kaya da Haidar suka yi

gidansa.

Dakinsa suka wuce da shi suna budewa kamshi

ya bige su ko ina a gyare fes kamar yana nan.

Jawahir ta hado

musu abubuwan ci da na sha suka ci suka sha

suka yi kat, sannan suka yi musu sallama tare da

kara yi musu addu’ar samun sauki. Jawahir ta

shige tolet dinsa ta hada masa ruwan wanka a

baho ta zuba turaren wanka a cikin ruwan nan da

nan turirin kamshi ya rinka tashi. Ta fito daga

tolet din ta durkusa Yaya ga ruwan wanka can na

hada maka, ya ce yauwa Babyna na gode.

Ya mike ya shige tolet dinshi kansa kamshin da

tolet din yake yi dabanne. Yana shiga cikin ruwan

ya ji wani dadin ni’ima ya ratsa shi ya fara

wankan.

Jawahir kuwa ta fito masa da wasu kananan

kaya, wando je three Quarter (tiri kwata) da rigar

50 Cent marar hannu ta kara feshe su da turare.

Ta debo masa mayukan da zai yi amfani da su

da turarukan. Ta ja masa kofar dakin ta sauka

zuwa kasa nata dakin. A lokacin kuma Kausar ta

dawo ko daga ina take oho ita ta sani.

Jawahir ta shiga wanka ta fito ta gyara jikinta

sai zuba kamshi take yi kamar wadda aka yi barin

turare a jikinta. Riga da wando ta saka da hula

mai harafin sunanta. Fuskar nan tata sai sheki

take yi, jikinta sumul-sumul gwanin sha’awa

kirjinta ya cika fam, da na shanu.

Ta bude kofar ta fito Haidar yana kwance a

doguwar kujera da karamin kur’ani a hannunsa

yana karatu. Kausar tana kujera me zaman

mutum daya tana zaune da jarida a hannunta

tana dubawa, kamshin da suka ji ne ya sa su

saurin dago kai Kausar ta saki tsaki ta mai da

kanta ga karatunta.

Jawahir ta wuce kicin ta dauko kofin gilas me

kyau ta bude firji ta dauko robar ruwa ta

Highland ta iso gaban kuherar da Haidar yake

kwance ta zauna a kasa kan kafet ta balle bakin

robar ruwan ta tsiyayo ta fiffito da magungunan

ta mika masa, “Yaya ga magungunan.

Ya dan mike zaune ya karbi magungunan ta

watsa bakinsa ta kafa masa kofin a baki ya sha

ruwan ya ce ta dan danna masa kafafuwansa don

ciwo suke yi masa. Ta mike sannu a hankali ta

rinka mamnatsa masa tana yi masa tausa. Jin

dadin tausar da ya jine ya sa shi fadin wash,

wash a hankali tare da lumshe ido.

Ita kuwa Allah sarki sai ce masa take yi sannu

sannu yaya cikin alamun ban tausayi, shi kuwa

taushin fatar hannunta mai kama da atafa shi

yake neman dimautar da shi, har yana neman sa

shi ya fita daga hayyacinsa, ba dan yana gudun

kada girma ya fadi ba ai da ya rungumota.

A ka kwankwasa kofar falon jawahir ta kalli

Haidar da yake kwance yana lumshe ido don jin

dadin tausa ta ce, “Yaya na je na bude kofar.?

Kai kawai ya iya daga mata don maganar ta ki

fita kanta bude kofar ta ja da baya don ganin

Yagwalgwal ce. Jawahir ta durkusa kasa ta

gaishe ta, ta ce “Munafuka ba zan amsa gaisuwar

taki ba, me kike jira a gidan da baki tafi ba tun da

kiyayyar da kike yi masa har ta kai ki sabauta

masa lafiyarsa ai za ki iya kashe shi ma, don

haka ni gaskiya ban yarda da wannan auren naku

ba ka sake ta kawai na gaya maka ba na son

gayyar tsiya gayyar jarabawa.

Jawahir ta fashe da kuka ta kalli Haidar ta ce,

wallahi ba don na riga na yi wa Dadyna alkawarin

ba zan kuma fita daga gidan nan ba, ba tare da

izininka ba wallahi yau da na bar zaman gidanka.

Ta durkusa a gabansa tana kuka, “Yaya don Allah

don Annabi yaya ka taimake ni ka sake ni ko ni

ma na samu sukuni a zuciyata.

Haidar ya sunkuya ya dago jawahir ya hada ta da

kirjinsa ya rungumeta yana shafa bayanta alamar

rarrashi, ransa a bace zuciyarsa ta yi bakikkirin

sai fat-fat take yi kamar ta fasa kirjinsa ta fito

waje. Ya kalli Yagwalgwal ya ce, “Yagwalgwal ina

ganin girmanki kada ki bari kimarki ta zube a

idona, jawahir ‘yar uwata ce ko ba aure a

tsakaninmu ni me rike ta ne ballantana matata ta

sunna ki rika aibata ta a gabana, ai aurena da

jawahir mutu ka raba takalmin kaza.

Yagwalgwal ta kama salati tana tafa hannu,

“Yanzu dan nan ni kake gayawa haka a kan

wannan mai kama da sadakar yallan kake neman

zagina, to bari na je wajen uban naka in kai ban

isa da kai ba ai shi ba zai ki jin maganata ba, tun

da ni na haifeshi ko. Jawahir ta zame jikinta daga

jikin Haidar ta nufi dakinta tana kuka ta rufe

kofarta. Haidar ya kamo hannun Yagwalgwal ya

ce, “Yi hakuri matar ta karfen na san du kishi ne

yake dawainiya da ke, Ta doke hannunsa ni sake

ni me kuma za ka gaya min bayan ka gama yi

min rashin kunya. Ya dada kamo hannunta yi

hakuri zo mu je sama dakina na gaya miki komai

don ki ji yanda abin yake. Da kyar ya shawo

kanta suka hau samansa suka zauna a falonsa,

duk wannan abin da ake yi Kausar tana zaune a

kujerar da take tana kallonsu kawai ba tare da ta

tofa komai ba.

Haidar ya ce da Yagwalgwal “Wallahi yarinyar nan

jawahir tana da mutukar hakuri ga ladabi da

biyayya ga sanin ya kamata da hangen nesa, tana

aiki da ilimin da Ubangiji ya ba ta, idan aka ce za

a yi ta tafiya a yanda a ke yi yanzu, to hakika

hakurin jawahir zai iya kai ni wuta.”

Yagwalgwal ta ce, “Dakata! Don na ce ka rabu da

ita kake kawo min wannan bayanin, ka je kada ka

sake ta ran da ta kashe ka ai ma zo mu dauki

gawarka ko?

Haidar ya ce, “Dole dai sai na fasa miki tarihinmu

za ki yarda da zancena. Haidar ya faro mata irin

tsanar da ya yi wa jawahir tun daga farko da

yanda har a ka yi auren da irin zaman da suka yi

da dalilin da ya sa jawahir barin gidansa har

kawo yau.

Yagwalgwal ta saka salati tana cewa, “Ashe ni

balokokon vanza nake yi kai ne marar gaskiya?

To wallahi ka kula ka rike ‘yar uwarka da kyau

don tana yi maka son gaskiya. Da haka dai suka

yi sallama ya debo kudi me yawa ya bata ta yi

masa godiya tare da sa masa albarka ta ce kuma

za ta zo ta bawa jawahir hakuri idan ta wuce.

Haidar ya juyo daga rakiyar Yagwalgwal ya

murda kofar dakin jawahir ya shiga, kamshin dadi

ne suka buge shi ya sheka ya karasa cikin dakin.

Tana zaune a gefen gadonta hada kai da gwiwa

tana shasshekar kuka, ya zauna a gefen gadon ya

dago ta ya kara ta da jikinsa ya rungume ta,

“Subhanallahi wannan jiki haka mai taushi da

dadin kamshi kamar atufa, Ubangiji ka nuna min

ranar da zan mallaki komai na yarinyar nan da na

nuna mata tsantsar soyayya da kaunar da ba a

taba nunawa wata ‘ya mace ba.

Duk zancen nan a zuciyarsa yake yi wanda har

ya so ya shagala cikin tunanin kyan kirar jawahir.

Sautin kukanta ne ya dawo da shi hayyacinsa.

Cikin taushin murya da magana kasa-kasa kamar

mai rada yake rarrashinta yana dan bubbuga

bayanta, “Sorry Babyna yi shiru haka kada kanki

ya zo yana ciwo kin ji baby na yi hakuri, ta dada

shagwabewa tare da langabewa a jikinsa tana

kuka kasa-kasa cikin sigar kissa da shagwaba

kukan nata me shiga rai da tsayawa masoyi a

zuciya.

Tuni kirjin Haidar ya fara bugawa fat fat,

“Subhanallahi ya salam wai yaushe zan mallaki

wannan tsantaararren jikin mai kama da robar

balo-balo?

Muryarta ya tsinkaya cikin rauni da taushi da

dadin murya tana cewa, “Yaya ka sake ni na

koma gida tun da kakarka ba ta son na zauna da

kai.”

Haidar ya ce, “A’ uxubillahi kada na kuma jin kin

furta wannan kalmar kin ji ko, don ubangiji yana

tsinewa duk matar da ta nemi mijinta da ya sake

ta, kada bacin rai ya sa ki rinka jawowa kanki

fadawa cikin fushin ubangiji kin ji ko? Yi saurin

yin istigifari.”

A hankali ta bude baki ta rinka nanata istigifari,

ya ce, “Yauwa Babyna Yagwalgwal ta ce a ba ki

hakuri. Zumbur ta mike ta shiga tolet don ba ta

son maganar don ita a zatonta tanda Yagwalgwal

take tsanarta da nuna mata kiyayya ba za ta taba

son ta ba.

Haidar kuwa binta ya yi da kallo komai nata sha

awa yake ba shi komai na jikinta burge shi ya ke

yi, wai shi ya zai yi da wannan zazzafar kaunar

da yake yi wa jawahir ne? Ta yaya zai yi ya

shawo kanta su kwanta gado daya ne da shi?

Duk dai da tanxu ba shi da karfin gaban da zai

tabuka mata wani abu to amma ko wasanni da

sun yi shi da ya ji ta kwance kan kirjinsa yana

wasa da wadannan tantsa-tantsan na shanun

nata(nono).

Duk dai da shi ya yi wasa da damar da ya samu

tun farko.

Ya dade a zaune yana zaman jira shiru-shiru

jawahir ba ta fito ba dole ya mike ya fita, tana jin

fitarsa ta fito ta sawa kofarta mukulli. .

Abu wasa-wasa jawahir ta kwana ta wuni ba tare

da ta fito Haidar ya ganta ba ko ta yi saken

kofarta a bude ya shigo. Sai dai wani abin

mamaki da safe za ta hada masa lafiyayyen

break a kicin din wajenta sai ta leko falon ta ga

ba kowa sannan ta jere masa kayan break din ta

kuma ajiye masa maganin da zai sha na lokacin

da robar ruwan Highland ta koma bangarenta ta

kulle kofarta, sai dai in Haidar ya gama shirnsa

ya sauko kasa ya hau tebir ya yi break ya dauki

magani ya sha ya jira ko jawahir za ta bude ya ji

shiru ya taba kofarta ya ji ta a kulle. A lokacin ya

juya ya koma sama sannan ya tashi ‘yar mulkin

tasa wato kausar sarkin ‘yan hutu, to wani abin

mamakin duk da yau kusan a falo ya wuni amma

be ga jawahir ta fito ba bare ya kalli idonta ya ga

yanda ta kwana. Sai da ya ji an yi kiran sallar

azahar ya daura alwalla ya fita masallaci amma

kafin ya dawo jawahir ta fito ta jere masa kayan

abinci, tuwon farar shinkafa ya tuku ya yi mulmul

da shi da miyar agushi, wadda don dahuwa kazar

da take ciki duk ta narke ta dagargaje a ciki.

Ta gasa masa naman rago mai ruwa ruwa ya sha

kayan kamshi ga tumatir da albasa kai dai

kamshi yake tashi. Sai lemon aya da ta hadawa

kanta ta zuba masa a jek ta cilla kankara ya sha

kayan kamshi, ta jere komai cikin kayatattun fulas

masu kyau ta sa farin kyalle mai dauke da

falawoyi a jiki ta rufe ta yi saurin juyawa ta koma

dakinta ta rufe sashenta ta shiga kicin dinta duk

ta gyara kayan data bata, ta wanke komai ta

goge ta mai da shi inda yake, sannan ta shige

tolet dinta ta saki shaya a kanta ta fara wanka. Karfe

biyu da rabi Haidar ya shigo gidan da carbi a

hannunsa, “Yan matan kausar ya ga daya a bakin

kofar falon tana gadin falon ta yi masa sannu da

zuwa ya wuce. Ya shiga falon ya taba kofar

jawahir a bame kamar yanda ta kwana. Ya

girgiza kansa kawai, shi jin kansa ya hana shi

kwankwasawa ya nufi bangaren kausar tana

zaune a kan kujera ‘yan matanta biyu suna

gefenta daya tana yanka mata tufa a kan filet

dayar kuma tana zuba mata abinci a daya filet

din, wanda ya kasa banbancewa da kuskus ne ko

burabusko. Yanda ya gan shi a dundunkule ya

sha ruwa ya yi sharkaf.

Ya zauna gefen ta ‘yan matan suka yi saurin

nikewa suka yi waje. Kausar ta dauki filet din

abincinta za ta fara ci ta kalle shi ta ce,

“Bismillah.” Ya ce, “Wa! Ni?

Allah ya sauwake na ci wannan abincin, ai sai na

yi amai.” Ta tabe baki ta ce, “Au kai fa ba ka cin

abincin masu aiki ko? Ka sa kanka a wahala don

yau na ga abin da za ka ci tun da na ga

Sarauniyar taka fushi take yi bare ta zo ta girka

maka.

Wai ni kuwa yau ka yi break? Don ban ji motsinta

ba bare na ji ko ta girka maka

Ya ce, “Ke za a tambaya ba tare muka kwana ba,

tsakanin ke da ita wa ya kamata ya yimin girki?

Ta tabe baki, “Ka san ni ban tashi a cikin wahala

ba don haka ba zan iya wani aikin komai ba.

Da kake maganar da ni ka kwana ai tausaya

maka na yi nake taya ka kwanciya don kada ka

kwana kai kadai, me kake iya tabuka min? Ka

riga ka zama nakasasshe, in ban da ka ishe ni da

tabe-tabe ka tayar min da hankali babu biyan

bukata.”

Ya daka mata tsawa tare da nuna ta da dan

yatsa, ke saurara kada ki sake ki kawo min

maganar banza a nan, da haka nake? Ko don

lalura ta same ni za ki gaya min maganar banza,

daure ki na yi ko cewa na yi dole ki zauna idan

kin gaji ba dole, ba zan danne miki hakki ba ga

hanya nan sai ki san inda dare ya yi miki.

A ranta ta ce, “Ba inda zan je gwarzon namiji

kamar ka ina zan iya barin ka, idan na yi sake ka

subuce min ta yaya zan yi na mayar da kamar ka

bare yanda na dandani zumarka ai sai dai na ga

ba ka samu lafiya ba tukunna zan ki zama da kai.

Ya gama banbamin fadansa ya fice yana tunanin

tsananin hakurin jawahir da kawaicinta. Ya ji

sallamar Hafsan faruk ya amsa mata cikin fara’a

yau ina megidan naki na gan ki ke kadai? Wallahi

yana office ka san bai taso ba, yanxu ma gidan

yini zan je ya ce na fara biyo wa na ga jikin naka.

Haidar ya ce, “Jiki Alhamdullahi.” Ta zauna a

falon suka gaisa ta ce, “Ina matan gidan ne? Ya

ce, “Bari na kirawo miki su. Ya kwankwasa kofar

jawahir ya ce, “Ki fito kin yi bakuwa, Hafsa ce ta

zo.

Ya juya ya nufi dakin kausar ya ce ki zo kun yi

bakuwa, “Tace, “Wacece?”

Ya ce, “In kin zo kya gani, “Ya juya ya fita. Jawahir

ta bude falonta ta fito cikin dammamiyar riga

body hook da jeans din wando da ya dame mata

cinyoyi daga kasa kuma yake da fadi, kanta ba

dankwali sai kananan kalba da ta tufka ta a

bayanta ta kwanto guda biyar gaba. Ta yi kyau

sai zuba kamshi take yi ta taho da dan gudunta

ta fada jikin Hafsa tana dariya. Haidar kuwa ya

zuba mata ido kallon ta yake yi yana hadiyar

yawu, yarinyar nan kuwa ta san yanda take rikitar

masa da hankali? Ta san yanda kirjin nan nata

yake dauke masa hankali kuwa?

Kausar ta shigo tana yatsina kujerar da Haidar

yake kai ta nufa ta zauna masa kan cinya ya ce,

“A’a ke me ye haka? Ta ce, Haba Darling kai ma

ka san nan ne wajen zamana don ka riga ka

sabar min.

Ya ce, “Amma kina ganin bakuwa a wajen ko? Ko

dan rashin kamun kai.” Ya zame ta takaici da

tsantsar kishi suka tokare zuciyar jawahir kamar

ta yi kuka ta dan daure ta ce, “Hafsa tashi mu

koma daki. Hafsa ta mike yayin da take gaisar da

Kausar. Suka shiga dakin jawahir Hafsa ta ce, tab

amma kina shan kallo, haka Kausar din take ba ta

da kunya? Jawahir ta ce, “Ina ruwana da ita? Me

ya dame ni da ita? Tun da ba zamanta nake yi

ba.

“Yanzu haka za ki zuba mata ido tana iskanci? In

ni ce ai sai na nuna mata cewar ita karamar ‘yar

iska ce, bare yanda na ga hankalinsa da

tunaninsa duk ya raja’a a kanki me ya sa ba za

ki sakar masa jiki ku rinka farantawa juna rai

ba.?

Jawahir ta ce, “Kyale ni Hafsa ni na san halin da

zuciyata take ciki a kan son Haidar, to kin san

wani abu da yake damuna? Na tsani na bude ido

na ga Kausar tana yi masa magana ko tana

kallonsa bare ta hada jikinta da shi wallahi sai na

ji kamar na je na shake ta ta mutu ko na huta.

Hafsa ta ce, to bari na ba ki shawara wallahi

yanzu yanda na fuskarki mijinki yana tsananin

sonki mai zai hana ki fito masa da taki irin kissar

kin san Allah nan gaba sai kin dinga tausaya

masa don bin ki zai dinka yi kamar rakumi da

akala saboda ‘yar uwa ba dama ce fa ke, dole ne

ki rikita Haidar, irin wannan cika haka komai ya ji,

me zai hana hankalin Haidar tashi da gigicewa a

kan ki.?

Jawahir ta ce, “To ai ni ba ki sani ba kunyar hada

jiki nake yi da shi sabo da sai na ga kamar zai ce

min ba ni da kunya.

Hafsa ta ce, “Tabdi jan zauna a barki a baya, au

na gaya miki cikin dabara da hikima za ki rinka

sakin jiki da shi kina yawan zama a duk inda

yake ki rinka yawaita kwalliyar da za ta rikitar da

shi kamar irin wannan sai kin zo kina ba ni labari

da bakinki, “Hafsa ta yi zumbur ta mike bari na yi

sauri na leka gidan wunin nan na koma gida kada

Oga ya dawo daga office ba na nan.

Jawahir ta yo mata rakiya Haidar yana falon tayi

masa sallama Hafsa tana gaba jawahir tana biye

da ita Hafsa ta fita daga falon jawahir za ta fita

ke nan Haidar ya yi magana kasa kasa, “Kada ki

fita harabar gidan nan da direba suka xo kada ya

ganki. “Jawahir ta ja tunga suka karasa sallama

da Hafsa tare da yi mata alkawarin zuwa in an

kwana biyu, ita kuma ta tafi.

Ta juyo daga rakiyarta har ta isa kofar dakinta

ya kirawo ta. Jawahir ta tsaya kam, a wajen ba

tare da ta juyo ba ta ce na’am, ya lankwasa

murya ya a raunane ya ce, “Yanzu haka za ki bar

ni na wuni da yunwa bayan kin san ba cikakkiyar

lafiya ce da ni ba, ga shi lokacin shan maganina

har yana kokarin wucewa, ta juyo a raunane cikin

tausayawa ta ce, yanzu ba kaci abinci ba.?

Ya dada langabewa to wa zai ba ni? Ke da kika

san ciwona kike girka min yanzu gashi ba ki yi

min ba. Ta ce, yaya na girka maka mana ta nufi

tebir din ya biyo bayanta yanda ta ajiye haka

yake ba wanda ya taba. “Ta bude komai ta jawo

filet ta fito da tuwo malmala biyu ta cire su daga

cikin ledar da ta zuba a filet din, ta zuba masa

miyar a daya filet din ta tura masa gabansa

kamar mai jira ya fara ci ta tsiyaya masa kunun

aya, ya yi sanyi kuwa karara a gilas kof ta ajiye

masa a gefe. Ta dan langabe kai ganin ya ture

filet din tuwon ta ce, duk yunwar da kake ji dan

wannan za ka ci? Ni jira nake fa ka cinye na kara

maka wani. Ya ce, “Haba Babyna na cinye

malmala daya da rabi ai dole na ji na koshi.

Ta dan marairaice cikin shagwaba ta ce, to ci

naman.” Ta bude masa kamshinsa ya bige shi

har na ji yawuna ya tsinke, ya kamo ta ya zaunar

da ita a cinyarsa to zauna mu ci tare don na ga

alamar ba ki ci komai ba.

Ta langwabe a jikinsa ta ce, “Uhm Yaya na ci

abinci fa a koshe nake.”

Ya ce, to gaya min me kika ci?

“Yaya na sha yogourt da nama na kuma sha

wannan. Ta nuna kunun ayar, da yake kofin. Ta

dauko ta sa masa a bakinsa yaya kai ma dan sha

ka ji akwai dadi. Ya kwankwada, “Uhm akwai

dadi, dan karamin, ta noke tana yi masa dariya

kasa-kasa ta ce, “Yaya ka ci naman tukunna

kada ka cika cikinka da ruwan kunun aya.

Ta yago naman ta sa masa abaki ya kama

taunawa yana lumshe ido um carkwai wannan

dadin haka kada ya tsinken kunne, “Ta kama

shasshekar dariya tana langabewa a kirjinshi tana

yago naman tana ba shi a baki.

Duk abin nan da ake yi dauriya kawai yake yi don

halin da jawahir ta tsunduma shi gaba daya ba

shi da wani kuzari ta dada rikita shi da kaunarta

da sha’awarta ta mamaye kowacce gaba ta

jikinsa, ta mike yaya ka ji ana kiran sallar la’asar

mu je mu yi sallah. Ya ce, to babyna na gode

Allah ya saka da Alkhairi Ubangiji ya yi miki

tukuici da gidan aljanna. Mu je na raka ki dakinki

ko babyna ta langabe a gefensa yaya kada a

tayar da sallah a masallaci ka je ka yi alwalar.

Ya ce, “A’a yau a tolet dinki zan yi alwalar ta yi

dariya to Yayana mu je.

Yau dai a dakinta ya yi sallah don shi ya ja musu

jam’i, ya dade yana kwararo musu addu’a sannan

suka shafa. Yau dai wuni guda cikin farin ciki da

annushuwa suka yi shi, gaba dayan su kokarin

farantawa junansu rai suke yi bugun kofar da ake

yi musu ne kamar za a balla ya sa Haidar saurin

mikewa cikin fushi ya je ya bude, Kausar ce a

tsaye tana girgiza kugu tana taunar cingam tare

da yamutsar fuska, “Lafiya.?

Abin da ya ce mata kenan.

Cikin tsiwa ta ce, “To me za ka yi min ko ka

manta cewar yanzu kai ba cikakken namiji ba ne

ka zama miskini? Ai ni ba ka da amfani a wajena

ita ma da ka ga tana rawar kafa don duk haka

kuke ne ita ma ba me lafiyar ba ce don haka ta

nakasta ka

Ya daka mata tsawa, “Ke kausar ki shiga

taitayinki ni ba sakaran namiji ba ne, ba ki isa ki

wulakanta ni ba.

Ita ma ta hau shi da ma sifa to ka sake ni mana

haka kawai don zalinci ka ajiye ni ka san ba iya

biya Min

bukatata za ka yi ba, kana so da aurena ne na

rinka bin maza kome kake nufi?”

Ya ce, “To shi ke nan na ji ki yi hakuri zan yi

shawara.

Ta ce, “Ina son zuwa gidan kawata. Ya ce, “A

dawo lafiya amma ki dawo da wuri tafi da direba

can sai ya kai ki. Ta juya ba tare da ta ce masa

komai ba.

Kausar tana daukar mota ba ta wani tafi da

direba ita kadai ta yi tafiyarta ta nufi gidan wata

kawarta, ita ma ‘yar Abuja ce aure ne ya kawo ta

nan kano.

Saddika ta tare ta da murna kausar amare yau

nake zancen mun kwana biyu ba mu hadu ba, ina

so in je gidanki ashe kina tafe. Ina angon naki ya

barki kika taho ke kadai.?

Kausar ta dauki lemon da ta ajiye mata ta kurba

ta ajiye ta ce, kyale angon nan nawa ai ni na

kusa barin gidansa. Saddika ta dafe kirji, “Haba

kausar me ya yi zafi haka? Ki tuna irin wahalar

da kika sha kafin ki samu Haidar ya amince ya

aure ki, yanzu idan kika rabu da shi ta yaya za ki

maye gurbin gayen yaro mai jini a jika da naira

kamar Haidar?” Kausar ta tabe baki tare da yin tsaki ta ce, “Ai

wadannan abubuwa da kika lissafa duk sun tashi

a banza don yanzu ya zama solobiyon namiji ba

abin da yake iya yi wa mace.

Saddika ta ce cikin razana, “Ban fahimce ki ba,

me kike nufi?

Kausar ta ce, lokacin da na auri Haidar na same

shi gwarzon namiji me cikakkiyar hallita wanda

ya iya jiyar da mace dadi ko ta ina ban taba

zaton zan iya rabuwa da Haidar ba don ta ko ina

ya yi min

Zamzam ga shi hadadden miji na nunawa sa’a, to

dan bakin cikin matarsa ganin ba ta da lafiya

komai bai taba gudanuwa a tsakaninsu ba shi ne

ta yi min bakin ciki ta kwada masa abu a

gabansa ta nakasta shi har kwanciya ya yi a

asibiti amma likita ya ce ai ya riga ya nakasta.

To yanzu ya dawo gida sai dai in mun kwanta

waje daya da shi ya ruda min jiki da wasanni ba

ya iya aikata komai wallahi ni na gaji gwanda ya

sake ni na huta.

Saddika ta ce, “Gaskiya yarinyar kamar ki da

kuruciyarki da komai zaman hakuri bai kama ki

ba, to amma ba kya tunanin wata rana zai samu

lafiya ki zo kina takaici?

Kausar ta ce, “Ke kuma kin ji ki da wata magana,

likita fa ya ce min ba shi da wata ranar samun

lafiya kina so na shiga yawon bin maza da

aurena ne?

Kinsan ko musulunci ya zama dole ya sake ni.

Saddika ta ce, “Gaskiya ne da ki cilla kanki a

halaka gwanda ku rabu kawai ki auri Bomboy ………… to amma ba kwanaki na ji kin ce

kina da ciki ba.”?

“Ba ciki ba ne ashe batan wata na yi daga baya

na ga al’adata ta zo. A nan ta yi sallar magariba

suka ci abinci ta yi sallar insha sannan ta tafi

gida.27

Related Articles

Leave a Reply

Check Also
Close
Back to top button

You cannot copy content of this page

Adblock Detected

YOU ARE USING ADBLOCK TURN IT OFF TO COUNTIUE BROWSING OUR WEBSITE