WAYE ANGON CHAPTER 1 BY MARYAM JAFAR KADUNA

WAYE ANGON CHAPTER 1 BY MARYAM JAFAR KADUNA

 

WAYE ANGON?

Rafi’atu ta shizo dakin hannunta rike da plate din

abinci, hannu daya kuma z06o ne a robar ruwa da

ake durawa guda biyu sun dauki sanyi karara.

Tabi inda Mabaruka take kwance da ido ta zauna tare

da aje plate din ta ce “‘Mabaruka!” Shiru bata amsa ba.

Ta kara kiranta ” Nasan idonki biyu ki tashi.” Ta tashi a

zaune a kasalance, kallo daya za kai mata ka gano bata www.dailynovels.com.ng

cikin walwala, ta dauko dankwalin da ya cire a kanta ta

yafa ta dubi Rafi’atun ta ce “Menene?”

Kallonta take tsaf! don son gano wani abu, sannan ta

ce

“Wai meye haka Mabaruka? Kina son damuwa tai

miki yawa ko?”

tayi mata shiru. Ta ci gaba

“Ki

saukakawa kanki don cuta bata da wuyar shiga jikin

mutum wallahi.”

Ta yatsina fuska tanakallonta, ta ce

“To me nayi

kuma?” Ta ce cikin kulawa,

“Ba ki komai ba, amman

kwanciyar da ki kai ba bacci ki ke ba illa tunani da kuka,

tun da na-fita na bar ki a haka na kuma taras da ke a

haka

Ta sunkuyar da kai ba tare da ta ce komai ba. Rafi’an

ta ce “Don Allah Ki daure Kawata ki barwa Allah komai.

ke dai kici gaba da addu’a kurum

Ta dago da tsumamman idamunta Kamar zata yi kuka

tace “To me kike so nayi? Kwana biyu fa ya  rage www.dailynovels.com.ng

Tayi

jim sannan ta nisa ta ce

“Na sani Mabarika, amman

na ce fa ki bar masa komai ki gane lokacinki bai

Kure ba

Ta ce, “Ke kadai ki ka zama matsalata Rati’a, Bacin haka

da tuni nayi nisa da garinnan, inda zan sami yanana da nutsuwva.” Tace, “Na gaji da jin haka Maburaka, kin fada

yafi a kirga, na ce miki babu inda za ki je wallahi.”

Ta buda baki zata yi Magana a kasalance ta yi saurin

katseta.

“Ya isa! Matso ga abinci muci muyi sallah,

sannan ma tafi.” Ta kalleta tace, *Ina kenan?”

Tana juya abincin ta ce, “Kasuwa mana, daga nan mu

sauka wajen Anti Farida muyi saloon din, Tun safe na

fad miki haka amman kin kasa rikewa

Ta dubeta da kyau tace. – Nima tun safen nake fada miki bazanjeba

“Wallahi ba ki isa ba, ya zama dole ki matso ma ki gani.

Muna da abubuwa fa da yawa Mabaruka?” Ganin bata

da shirin matsowan yasa ta haye saman katifar da

abincin ta mika mata cokali ta ce, “Karbi muci mu wuce,

yana hucewa ga lokacin sallah yana tafiya.

Ta makale hannu taki karba. Hakan yasa Rafiar ta

Daga murya ta Kwalawa Mama kira. *Mama!” Daga can www.dailynovels.com.ng

Tsakar gida Maman ta ce,

“Ya aka yi ne?”

Ta ce,

“Mabaruka ce mana.”

Jin haka yasa ta taso ta nufo dakin. Ta dubi

Mabarukan ta ce, “Ya aka yi ne?” Ta dago da jajayen

idanunta tana kallon Maman ta kasa cewa komai.

Ta dubi RafI’atun ta ce, “Ya aka yi ne?” Ta ce “Abinci

taki taci.

** Maman ta karasa wajen Mabarukan ta zauna

Gefen katifar ta ce -Ya aka yi ne Mabaruka don me bazakici abinci ba?” Ta ce a sanyaye “Bana jin yunwa ne.

Tace,

“‘To me yasa ko na safe fa banga kin ci wani abun

kirki ba, zama da yunwa illa ne, daurewa za ki kada

damuwarki ta shafi cikinki,

Hmmm yanzu aka fara www.dailynovels.com.ng

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button

You cannot copy content of this page

Adblock Detected

YOU ARE USING ADBLOCK TURN IT OFF TO COUNTIUE BROWSING OUR WEBSITE