WAYE ANGON CHAPTER 2 BY MARYAM JAFAR KADUNA

WAYE ANGON CHAPTER 2 BY MARYAM JAFAR KADUNA

 

Damuwa dai akwaita rashin cin abincin ba zai yaye

damuwar ba, illa ma ya Kara damuwa. Amman in kika ci

za ki samu karfin jikinki kuma damuwarki tayi sauki.”

Mama ta saurara.

Mabarukan ta ce,”Zan ci Mama ko zuwa anjima.”‘ Tace,

‘A’a ban yarda ba, yanzu nake son kici. Kinga zaku

je saloon ya kamata zuwa yau kin yi saloon din da lalle,

ga maganinki can a kan wuta anjima za a kawo y an shilar.Ta kalleta zata yi kuka ta ce,

“Duk meye amfaninsu WWW.DAILYNOVELS.COM.NG

Mama? Ni fa ba na farin ciki, don Allah ku «kyale ni da wadannan abubuwan

Mama tayi murmushi nasu na manya taCe

‘”‘Mabaruka kenan! Ita Amarya an santa da gyara da

kwalliya don angonta da mutanen da za su zo mata

murna su ganta fes! Gwanin sha’awa kowa ya yaba ya

gamsu lallai Amarya ce.

Amman idan ki ka tsaya a haka waye zai zo ya ce ke amarya ce? Kwalliya ya zama dole kiyi Mabaruka, kiyi

hakuri.” Zata yi magana Maman ta katseta “Ya isa!

Dauki ki ci abincin.

Ta jawo mata abincin a gabanta

tare da cewa “‘Oya maida hankali in ga kin ci da yawa.

Yawan musun ba shi da amfani bare ga babbar mata

wacce take ganin girmanta da Kima, uwa ce gareta. Don

haka ba don tana da bukatarsa ba ta fara tsikararsa ranta

cunkushe ba ya mata dadì sam! Ji take kamar ta fasa ihu

ko ta samu sauki.

Maman ta mike tana cewa,

“Yauwa Mabaruka!

Hakuri za ki ki ci abincin ku tafi kar kuyo dare.

» A can makoshi ta ce, “To.”

Bayan fitar Maman Rafia ta ce “Kin ji ko? Don

Allah ki saki ranki ko nima kin karfafa min gwiwa,

kowa da yanda Allah yake tsara masa rayuwa da

jarabarshi. Taki kenan a haka tazo miki, kar kiyi fushi ko WWW.DAILYNOVELS.COM.NG

ki ja da ikon Allah.”

Ta dubeta ta ce,

“‘Ke tunda ki ke kin taba ganin irin

haka tsakaninki da Allah?” Ta ce,

“A’a ban taba ganiba.

“‘ Ta ce,

“To da wane suna zan kira nawa auren? Ni ba

auren dole ba ko a garin mahaukata ba a haka, bare a

Musulunci wanda hakan babban laifi ne da hukunci mai

girma ga duk wanda ya aikata haka, duk saboda kafiya

irin ta iyayena da jahilcinsu kowa son ransa yake so.”

Ta ce, “Ya isa haka nan. Ki bar kiransu da haka, dole

dai akwai mafita a al’amarin nan, kuma za ki gani.Ta ce,

“To amman meye amfanin yin kwalliyar

Rafi’a? ban san wane matsayi nake ba, ban san wane

angon zan wa kwalliyar ba?”

‘” Ta ce, “Da duk wanda aka

riga aka daura shine zaki kaiwa kwalliyar.

‘Ta numtasa ta

ce, “Tir! Da halin iyayena, da yanzu na dade da kai

Kararsu kotu, amman aka hana ni.”

Ta ce, “Ya isa haka Mabaruka! Mu ci muyi sallar saimu wuce.

” Bayan sun gama sunyi sallah- sannan suka

fice.

Karfin shiga kasuwar daman a su kara tsintsinto

wasu abubuwan da ba a karasa saye ba, ba don son WWW.DAILYNOVELS.COM.NG

Mabaruka ba. Duk abin da Rafi’ar ta gani sai ta dauka,

suka yi shatar me Adaidaita ta cika dam.

Fitowa tayi daga shagon ta fito ta tsaya bakin motar,

sam! Ba abin da yake burgeta, ba abinda ta zabo don

ra’ayinta duk zaben Rafi’ar ne tamkar ita ce amaryar.

Ta fito ta sameta ta dubeta da kyau ta ce, “*Shi ne ki ka

fito ki ka bar ni da zaben ki ka dawo nan ki ka tsaya?”

Mabaruka ta yatsina fuska tana kallon wani wurin

daban. Ta ce, “Meye amfanin sayen kayan to, alhalin

ban san gidan wane angon za a kai ba, Sulaiman ko

Imran?”

Raf’ar ta ce, “Ko ma wanene kin san dai dole gidan

daya za a kai ki, ko Imran din ko Sulaiman, don haka ki

zage kawai ki dauki abinda kike so.”

Shigewa motar tayi ta zauna tana cewa, “In kin gama

ina nan ina jiranki, rana na dukana.”

Sakin baki tayi tana kallonta, sannan ta kada kai ta

koma shagon tana cewa,

“‘Allah ya shiryaki Mabaruka

Sai da ta gama daukar abinda zata dauka sannan ta

dawo motar suka shiga. A shagon saloon din Anti Farida

suka tsaya, ta ce wa Mabarukan ta shiga ta jirata ta kai

kayan ta dawo.

Mabaruka ta shiga shagon da sallama jiki a mace

tana jan kafa. Anti Farida ta bi ta da kallo har ta zauna, ta

ce “‘A’a amarya ya dai na ganki haka ba WWW.DAILYNOVELS.COM.NG kuzari, ko an

fasa kukan amarcin?”

Mabaruka ta zumburo baki taki cewa komai. Anti

Farida ta ci gaba da fadin «Yanzu nake shirin rufewa in

je in ji lafiya har yau ba ku zo ba, ina Rafi’atun?” Ta ce

ciki-ciki “Ta wuce gida ta dawo.

Ta kalle ta tsaf! Sannan ta dawo kusa da ita ta zauna

tare da data kafadarta, ta ce

“Menene Mabaruka?”

Mabarukan

ta kalleta idanunta sunyi kwalkwal.

Hankalin Anti Farida ya kara tashi ta ce.

«Fada min mana, ko an fasa auren ne?” Mabaruka ta ce,

“Da hakan yafi min dadì da kwanciyar hankali.” Anti

Farida ta ce cikin rashin fahimta.

“Kamar ya?” Ta ce a

marairaice zata yi kuka “Maza biyu fa ake kokarin aurar

da ni gare su.”

Cikin sauri Anti Farida ta zazzaro idanuwa ta ce,

HMMM LABARI FA NATA TAFIYA SHIN KOYA ZATACI GABA DA KAYAWA KUDAI KUCI GABA DA KASANCEWA DAMU A KODA YAUSHE WWW.DAILYNOVELS.COM.NG

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button

You cannot copy content of this page

Adblock Detected

YOU ARE USING ADBLOCK TURN IT OFF TO COUNTIUE BROWSING OUR WEBSITE