Yar tallah10
*YAR TALLA*
CHAPTER10
Dan iska wulakantacce Allah ya tsine maka Rabi’u banga amfanin rayuwar kaba.
Yanzu uwar taka ce zata mare ka har ka daga hannu zaka rama, don kana marar kunya lalatacce. To bari in tsine maka kaje can ka Karasa lalacewar ka tunda kai din ba dan mutunci bane, inba dan iskaba kishiyar uwa ba uwarka bace, k0 k0 hudubar da uwar taka ta tafi ta bar maka kenan? In banda na shigo da yanzu marinta zakai da gaske, « don kana marar kunya.”
Laure tasa kukan munafurci tana fadin, “Kuma Malam wai kan abin da bai taka kara ya karya ba yaron nan ya dinga marina har yana fadar shi zai zamo ajalina wai dan kawai na ce bai kamata ya sanya Saude makarantaba da kanshi ya bari har kazo yayi maka magana. Shi kenan yaron nan ya shiga zagina ta uwa ta uba wai har: yana fadar shi zai zamo ajalina….”
Ta Kara fashewa da kuka, ‘Wallahi Malam bazan iya zama ba yaron nan ya kashe ni a banza a wofi ba, wallahi tafiya ta zanyi in bar masa gidansu tunda yana da gaskiya gidan ubansa ne
Malam yace ‘Da Alla bar’ wannan magamar
Laure karma kija yaron nan ya Kara raina ki gidan ubansa, dawa ya fada masu, ni ubansune
yaranda akaimin wuru-aka manna min tsiya~
Ya juya yana kallon Saude da Rabi’u yana fadar, “Baku sanibane koba a taba fadi maku bane kama uwarku da kwarto Kiri-kiri akayi iyayenta suka koreta dalili kenan da yasa tabarku ta tafi yawon karuwanci yace wlh kukaci gaba da takuramin ko matata a shirye nake dana koreku daga gidannan
Rabi’u ya riqo hannun Saude suka nufi dakinsu suna shiga ya jingina kansa da bangon daki yana wani irin kuka maicin zuciya yake
Itakanta Sauden kukan take yanzutafara fahimtar suwayesu dakuma matsayinsu acikin gidan duk da qarancin shekarunta hakan bai hana ta fahimci dalilin tsanar da ake masu ba tasa hannunta ta riko hannun Rabi’ u tana fadar
“Wai Yaya da gaske ne abin da aka fada? Yaya
da gaske mahaifiyarmu karuwa ce muma bamu da iyaye?”
Rabiu: ya waigo yana kallonta hawaye sun gama bata masa fuska ya Kara riko hannunta yana
Yana girgiza mata kai cikin muryar kuka yace, “Karki soma wannan tunanin Saude nasan kowacece mahaifiyarmu donni na rayu da ita :nasan kowacece ita, ita din mutuniyar kirki ce knma ‘yar manyan mutane.
Saude tace, “Yaya idan har mahaifiyarmu mutuniyar kirki ce to me yasa ta watsar da mu ‘yan uwanta suka guje mu ta barmu mu kadai muna rayuwa cikin qunci da wahalar?”
Rabi’un yace, “Saude mahaifiyarmu na son mu kamar yanda kowace uwa ke san danta, dole ce ta rabata damu badan tasoba kiyi mata uzuri Saude duk qunci da wahalar da kike ciki bai kai wanda ita . ta shiga ba.” .
Saude tace, “To,amma ”
Ya daga mata hannu da sauri alamar baya son jin abin da zata fada, sannan ya juya ya fice ya bar mata dakin Wani kuka ya qara zuwar mata ta kwanta taci gaba kukan abinta. tanajin zuciyarta. na suyakamar garwashi,yamaza ai Rabi’u yace mata qarya ne abin dasu Baba da Laure suka fada a , kan mahaifiyarsu alhalin alamomi sun nuna gaskiyar
Shin idan har mahaifiyarsu tana son su me yasa ‘ ta tafi ta barsu babu k0 waiwaye? Shin idan mahaifiyarsu mutuniyar kirki ce me yasa ‘yan uwanta suka kore ta? Shin idan har ta tsare kanta me
Zaisa mahaifinsu ya zargeta harya kyamacesu da zama a matsayin yayansa?
Tambayoyin data jeroma kanta kenàn
Wanda bata da mai amsa mata su
1 page is missing am sorry
ya farkar da ita, don haka ta dauki kayan ta koma gida babu cinikin ko sisi.
K0 data maida alalen Laure tayi ta masifa ai tun da kika fita, “Na lura mugunta ce kawai yau kikasa mini
kuma ‘yar iska ke zata karewa a je min kayana ki.’ wuce
Saude ta samu ta ajiye kayan tayi daki da hanzarinta, don dama barci ne fal a cikin idonta ta samu ta kada kafadunta ta kwanta, wani bacci mai nauyi k0 yayi awon gaba da ita.
Inna Laure bata basu alalan ba saida gari ya ‘ waye a lokacin ta lalace sannan ta miqo masu ita waisu karya da ita. Rabi‘u ya kai ya zubar ya ciro kudi ya siyo masu koko da qosai suka karya, sannan ya tafi wurin aikinsa, Saude kuma ta tafi talla.
Da yamma likis Saude ta dawo daga tallar, Laure ta bata dakan kunnun jego wanda ta karBo a makotansu da akai haihuwa, kawai saboda neman suna, shishshigi cusa kai ba kwarjini. Saude na cikin dakan ta debi gyalenta ta fice ita da ‘yarta.
Suna fita Saude ta ajiye dakan ta kwanta bakin turmin tana hutawa a lokacin Rabi’u ya dawo daga ‘ wurin aikinsa shima ya kwaso gajiyarsa ya zauna kusa da ita cikeda tausayawa yace, “Sannu ya jikin naki ne?”
Saude tace, “Da sauqi sai dai ciwon kirjin da ya matsa mini yanzu.”
Rabi‘u yace, “Allah ya sauwaqe karbi wannan bari inje chemist na siya miki magani.” . Saude tayi saurin sa hannu ta karBa tana: dubawa leda ce baqa guda sai farar leda guda. Ta bude: soyayyar doya ce da kwai a ciki, dadi ya kama ta yanzu: itace zata ci doya da kwai. wanda tunda take a duniya bata taba cinta ba. Ta yi saurin kallonsa da Washe fuskarta tana fadar.
“Wayyo Allah na Yaya, yau zan ci doya, tunda nake fa ban taBa cin taba wallahi.”
Rabi‘u yayi murmushi yana kallon ta, sai daya tashi zaibar wurin sannan ta bude baqar ledar. Tayi wani tsalle
ta tashi tana fadar.
“Wayyo dadi, Yaya kayan kwalliyana ne?” Ya daga mata gira, ta buga wani uban tsalle ta dafa shi taba fadar.
“Wayyo Yayana na gode kwarai wallahi dama ina so nima in rinka lrin kwalliyar su ‘Yar Baba, inyi; kyau k0 Yaya?”
Ya daga mata kai alamar eh, tasa dariya ta ciro madubi tana kallon kanta tana ta faman gwalegwalen idanuwa.
“Kai Yaya wai dama haka nake, Yaya kalli idanuwana ‘yan qanana-qanana, yanzu kuma Yaya wannan bakin nawa har cokali yana iya shiga ciki?” Ya buga hannun shi saman tafin hannun shi alamar oho tayi daria
Tace yaya ji haqorina har yayi tsaho da yawa’
Rabl’u ya kwace madubin yana fadar, “Ke tashi kiyi aikinki
saude ta shagwabe masa “kai Yaya don Allah ka bari in gani wallahi ban gama ganiba
Rabiu ya saka madubin cikin ledar yana fadar, “Idan kin shigo daki kin gani ai naki ne bana wani ba, kyata gani harki gaji. Dauki doyarki ki ci kinji
Ta ture doyar can tana turje-turjen qafafuwa, Rabi’u ya dauki doyar yana fadar, “bazakiciba ke nan to bari in cinye abuna dama ba qoshi nayi ba rago miki.” nayi
Saude ta yi saurin riqo rigar shi tana fadar. ‘Yi haquri’ don Allah ka bani na daina.‘
Rabi’u ya sakar mata ya wuce yana dariya, ta zauna tana ci tana lumshe ido har ta gama, sannan ta mike taci gaba da dakan yajinta iya qarfinta. Ta samu ta gama, sannan ta wuce daki ta janyo kayan kwalliyan tana duddubawa, ta zauna ta manne fuskarta radau da kwalliya abin kada sabon shiga, duk ta yi wa fuskarta dame-dame man da kwalli
Washe gari ma tana gama sallar Asuba ta janyo kayan kwalliyar ta hau ranbadawa a fuska, shi dai Rabi’u yana zaune yana kallon ikon Allah. Tana gamawa ta mike ta nufo shi tana fadar.
“Yaya duba ka gani wai nayi kyau?“
Rabi‘u ya yi wani takaitaccen murmushi kafin yace. “Sosaima, don sai yanxu na Kara tabbatar da kamar ki da Mamar mu daya, sak kamar an tsaga kara wallahi.” ‘
Saude ta gyara zama tana fadar, ‘Wai Yaya don Allah ya Mamarmu take, baqa ce k0 fara k0 doguwa k0 gajeriya?”
Rabi‘u ya yi murmushi kafin ya ce “Mamanmu fara CE fat don har ta fiki . kuma doguwa ce mai
Dan jiki kadan, yadda. Kika ganki haka take.”
Ta ce “To yaya tana son mu?”
Rabi‘u yace, “Sosai ma kuwa don ranar da zata
rabu damu tasha kukan fitar hankali keko saida a kai da gaske sannan aka Banbare ki daga jikinta kina ta tsalla da ihu a lokacm kina da shekara shida a duniya.” Saude ta yi wani murmushi kafin ta ce “To Yaya yanzu tana ina?” . Ya girgiza mata kai yama fadar, “Allahu a‘alamu.” Ta dan yi jim kafin ta ce “To Yata ” me akai mata data tafi ta barmu? Kafin ya kai ga bata amsa Inna Laure ta hankado
labule tana fadar, “To tif da taya ‘ talla sai a tashi a tafi tallah hakanan
Saude ta mike cike da alamun gajiyawa a
fuskarta ta fice ba dan ta so ba. Ta tafi tallar da ta zame mata waki’a farilla.
Da daddare ciwon mara hade da ciwon ciki mai tsanani ya rufe Saude tamkar ba za ta kai ba, ta ringa murkususu a tsakar daki ita daya a lokacin Rabi’u
bai dawo ba.
Laure na jin ta, amma k0 ta kula ta kanta. Haka Rabi’u ya dawo ya same ta hankalin shi ya yi masifar tashi, ya juya ya koma ya siyo mata magani ya bata, amma a banza, sumanta biyu cikin dare. Yanda suka ga rana haka suka ga dare daga ita sai Rabi’u cikin daki babu wanda ya leqo balle ya ji halin da take ciki, don Malam ma bai san abin da suke ciki ba.
Cikin ikon Allah ana kiran sallar Asuba, jini ya zowa Saude, a take kuma ciwon marar ya dauke, don haka ko motsi ba ta iya yi ba daga inda take ta kwanta sai bacci mai nauyi ya dauke ta.
Sai a lokacin Rabi’u ya samu kwanciyar hankali ya tisa ta a gaba ya rabka uban tagumi yana kallonta hawaye masu zafi suna biyo kuncinsa zuciyarsa ta cika da tausayinta, har gari ya fara haske sannan ya “farka ya mike ya je ya yi sallah ya dawo ya samu ya dan kwanta saboda baccin dake cike cikin ldanuwansa.
Cikin barcinsa ya ji tamkar ana rabka sallallami, Rabi u ya bude idanuwansa da su kai masa wani irin nauyi saboda bacci, ya ga Inna Laure na fadar
“Malam! Malam zoka ganewa idon ka ikon Allah Malam zo ka gani.”
Malam Bala ya fito daga dakinsa yana fadar, “Ni
ko kinsan banson irin wannan kiran na tashin ”hankali.”
Laure ta qara hankade labulen dakin sosai tana fadar, “Ai wannan idan ma akwai abin da yafi tashin hankali to shi ne dubi yarinyar nan Saude kalli siket dinta.”
Malam ya qara tura kai cikin dakin tsawon wasu ‘yan sakanni kafin ya ce ‘Kamar jini nake gani Laure?”
Laure ta turo wuya gaba tana fadar, “To duba da kyau jini ne daman tun jiya nake jin ihun yarinyar nan na dauka wani iya shege ne ashe yaron nan ne ya haike mata.”
Gaban Malam ya yi wani mummunar faduwa ya juya yana kallonta a razane bakinsa na fadar, “Ki bari don girman Allah.”
Laure ta tabe baki tana fadar, “Ga alama nan.”
Idanuwan Rabi’u suka yo waje don sai a lokacin
ya lura da yanda jini ya Bata siket din Saude sosai kamar anyi Barin manja a jikinta abin kaga kaya
masu haske da santsi, hankalin shi ya yi masifar dugunzuma.
Malam yace “Lallai kam yaran nan ka cika la’anannen Allah yau kam sai na gwada maka irin nawa rashin imanin ni zaka jawa abun kunya, ka yiwa qanwarka fyadeee dan iska to wlh daga rana irin ta yau ka gama haikewa ‘ya’yan jama’a.” Ya juya a zafafe sai ga shi ya janyo wani qaton faskare, Laure ta riqe tana
fadar. A,a don Allh kayi haquri Malam karka kashe shi.”
Malam ya goce yana fadar, ‘Wallahi yau sai dai akwashi gawarsa cikin gidannan inya so nima a kasheni yayi kukan kura gamida yin kansa da faskaren
*Wooooohoho jama,a wai ya abin yakene mu tara gobe daidai wannan lokacin donjin yaddah wannan taqaddama zataci gaba da kayawaaaaaa tare da niiiii*
*ABDULLAHI ISMAIL SALANKE*
Nake cewa GOBEMA da LABARI