Yar tallah28
YAR. TALLA
CHAPTER28
Kuyi haquri yau ban kawo maku akan lokaciba aikine yaimin yawa kunsan yau monday
Doctor Mariya ta rungumo Saudat a jikinta hawaye cike da idonta, tace
“Kiyi hakuri Saudat, ku yafe min, wallahi ban watsar daku ba don son zuciyata,ba sai don kawai ba yadda zan yi, amma yanzu nayi miki ‘ alkawarin zan baki duk wata kulawa ta uwa wadda kika rasa a baya”. ‘
Saudat ta lumshe idanuwanta hawayen da suka cika su suka rinqa zuraro wa cikin sanyayyar muryarta ta amsa da, “To Momy”. Kamar yadda taji su Nabila na ce mata.
Dr. Mariya ta dan zame jikinta kafin ta ce
’ “Tashi kiyi sallah kinji ana kiran magriba, ni
ma zan’shirya yanzu muje gidan Yaya Sani, don tuni nayi masa waya gamu nan zuwa”.
. ‘ Saudat ta amsa da to, Dr. Mariya ta mike ta‘
Fice Saude ta raka ta da idanuwanta har ta Bace,
wani irin tausayin mahaifiyarta ne ta keji, dan a
ganinta tafi shiga wahalar rayuwa. ”
Saudat ta mike ta nufl bandaki ta dauro alwala ’ta fito tayi sallah, sannan’ta mike ta nufi gaban madubi ta kara gyara fuskarta ta shafa hoda ta goga wa laBBanta man lebe mai danko, sannan ta gyara girarta ta tattada gashin idonta da
mascara, ta gyara nadin gyalen kanta sak ta fito tamkar wata cikakkiyar balarabiya.
Tana cikin fesa” turare ne a. jikinta Dr. Mariya ta shigo da sallamarta, a yanzu tana sanye ne da dogon hijabi milk kalar atamfar jikinta da makullin mota a hannunta, ta mika wa Saudat
wasu fararen takalma flat shoe masu kyau.
Saudat ta saka sannan suka jera suka fice, a falo ta hadu da ‘yar‘ aikinsu Mairo dattijuwa wadda ba ta wuce shekaru hamsin ba. Tana ganin ‘Saude ta hau gaishe ‘ta, kunya ta kama Saudat, ta gaza amsawa sai dai ta juyo mata da gaisuwar ta amsa cike da girmamawa sannan ta dubi Dr. Mariya tana fadar.
“Amma Hajiya qanwarki ce wannan ko, naga kamar taku tayi yawa”.
Dr. Mariya tai murmusa kafin ta ce
“Mairo kenan, yanzu nan har kin ga kamarmu?”
Mairo ta Kara wangale baki tana fadar.
“Sosai ma wallahi Hajiya, har wurin tsawon da basken fatar hancinku ma iri daya ne, ‘ wallahi sai ace kanwarki ce
Dr Mariya tasa dariya tana fadar.
“A’a lallai Mairo idanuwan nan naki har yanzu da Kwarinsu, to ‘yata ce, Yayar su Nabila ce . wadda na baro su kauye ita da yayanta, ai’ina jin‘ na ba ki labarinsu k0?”
Mairo ta zabura ta dafo Saudat tana fadar. .
Sannu baiwar Allah, ashe zan ganki ban ‘ mutu ba? Ai ko Hajiya wallahi ga kama nan ita da ‘ Nabil kamar danta ba kaninta ba, Allah sarki”. Dr. Mariya ta yi murmushi da jin tsokanar Mairo ta dubi Saude’ “Mu je kinji in dai Mairo ce bata gajiya sai tasa mu kwana anan”. ~ Nabila ta sarko hannun Saudat tana fadar “Don Allah Aunty zan je” . Kafin ta yi magana Nabil ma ya dafe ta yana fadar. ” ‘” “Nima don Allah Aunty aje dani’_’. Saudat tayi sukuti tana kallon fararen ; yaran ‘yan shamal-shamal dasu Dr. Mariya ta ce. “Kuyi haquri ba da Wanda za muje, kuje Mairo ta dauko muku Ice cream a firij”. . . Saudat ta langwaBe kai tana: kallon mahaifiyar tata, tace.“Don Allah Momy a je dasu; Mariya tayi murmushi tana fadar. Kunci arzikin Auntynku, oya, muje“ . Suka rungume Saudat suna ‘tsallen ‘. ~ murna, suka tafi cikin wata qaramar mota. Qirar End Of Discussion sabuwa dal, Dr Mariya ce ke. jan motar Saudat a gidan gaba, sai Nabil da:
Nabila a gidan baya. suna ta“ yan tsalle-tsallensu. ‘ Dr Mariya ta dubi Saude kafin ta ce
‘ “Oyoyo my sister, zomu shiga”.
Nabila ta dafo ta tana fadar.
“Aunty Shukura yau ba zaki dauke ni ba.”
Shukura ta janyo hannunta tana fadar.
“Yau ba take nake ba Nabila, ta sister nake ina dan Momy mai qaton kai ~ Nabil ‘da ya labe bayanta yana dariya ya
ruga wurin Dr. Mariya don ya san rankwashinsa
za ta yi. A haka suka shiga cikin qaton falon, inda Alhaji Sani yake zaune da matarsa Hajiya Fadila sai Yusuf da Abdulhakim duk qannen Shukura ne; suna shiga Hajiya Fadila ta nufo su da fara’a a
fuskarta ta riqo Saudat tana fadar
“Taho nan mu gaisa Saudat, sannu kinji” .. Saudat tayi wani murmushi ta durkusa tana gaishe su, Alhaji Sani ya mika mata hannu yana fadar. ” “Zo nan Saudat, z0 in ganki, taho kusa da ni kinji”. ‘ Saudat ta ja jiki ta har inda yake zaune, ya sa hannu ya dafa kanta yana kallonta cike da
. tausayawa yace
“Allah Sarki, ashe da rabon zaki gana da’ mahaifiyarku? Allah Sarki rayuwa kenan yanzu ni k0 za ”a, kashe ‘ni ina zan iya ganin wannan ince Saudat ce? Ai sai inyi zaton irin bakin larabawan nan ne wa zai ce wannan irin Bala ce?”
. Duka falon aka sa dariya‘ ban da Saudat, wadda ta sunkuyar da kanta tana wasa da kwalliyar rigarta. Shukura ta rankwafo ta wuyan
Saudat tana fadar.‘ ‘ “Me za,a kawo miki, ’fruit k0 snacks, k0 abu
mai nauyi?’ Saudat ta dan saci kallonta tana murmushi,
‘ ta ce. “Komai ki ka kawo . Shukura ta yi wani dan fari da ido, kafin ta
mike da kuzarinta Alhaji Sani ya dubi Dr: Mariya yana fadar. “Kin ga abin Allah k0? Ban taba kawo wa a raina yarinyar nan zata rayu ba, na mafi ganinta ‘ ga shi Rabi’un, saboda kinga shi namiji ne duk’ ‘ inda ya sa gaba zai iya rayuwarsa. Ki dai ci gaba da addu’ a shi ma Allah ya bayyana mana shi”.
Dr Mariya ta amsa da, “Amin yaya, amma da kamar wuya, saboda yaron fa korarsa uban ya yi da girmansa”, Alhaji Sani yace“Wannan maganar banza . ke nan, ki shirya kuje garin duk inda danki yake’ ya fada miki ai ba zai yiwu a uba ya kori da kuma yace bai san inda yake ba,ba sai muyi
kararsa ba idan ma sayar da shi yayi”. Ya dubi Saudat
“Amma ai ya barku kun wuce gaba da ‘ sakandire k0?”
Saude ta girgiza kanta cike da damuwa, kafin ta ce
“Ai ba a ma samu makarantar ba”
Mamaki, haushi da takaici suka kashe Alhaji Sani sai dai ba yadda zai yi, haka ya hadiye, yanzu a ce kana da kyakkyawar diya kamar Saudat idan baka sata makaranta tayi karatuba aikakasheta, kakashekanka.
‘ Shukura ta shimfida tabarmar lambawa ta jets gaban Saudat da kayan ciye~ciye da lashelashe abin harya soma bawa Saudat mamaki.
Saida suka yi da gaske sannan ta iya sakin‘ jikinta suka ci abincin dasu Nabila, basu suka bar gidan ba sai bayan sallar isha, bayan Alhaji Sani da Dr. Mariya sun ajiye magana jibi za taje har can kauyen da kanta. Shukura ta‘ makale ita
ma za ta, Alhaji Sani yace duk abinda kukai anan zan nemar wa Saudat karatu
Dadi ya cika Saudat yadda taga manyan mutane sun nuna mata kulawa da soyayya, har kukan dadi tayi a boye, don rashin Yaya Rabi’u kusa; da ita da taga irin tasa murnar da farin cikin, shi da yasan Momyn taSu ya zauna da ita, yazo yaga cikin daular da take
Saudat, ta qara juyawa da kwanciyarta saman’ lallausan gadon daya sha shimfidun alfarma, ta kalli gefenta inda Nabila ke kwance tana sharar baccinta don kuka tasa wai ita wurin ‘ Aunty yau za ta kwana ta bar Nabil tare da Mairo Yau Saudat tayi bacci mai dadi da nutsuwa, duk da Dr. Ahmad yayi wa zuciyarta kane-kane amma hakan bai hana ta bacci mai dadi ba.
Washe gari tunda tayi sallar asuba ta koma ta kwanta, sai da Mairo ta kwankwaso‘ qofa ta dauki Nabila za,a yi mata shirin makaranta, tana daukar Nabilar kuma ta maida qofar: ta rufe ta koma tayi kwanciyarta. Ba ita. ta farka ba sai qarfe tara daidai na safiya, tana tashi ta nufi bandaki ta watso ruwa ta fito ta maida doguwar rigarta tayi ‘yar sassaukar kwalliyarta sannan ta
zura takalminta ta fito falon gidan. ‘ ‘. Babu kowa a falon sai Mairo da keta faman goge-gogenta, Saudat ta dan duqa ta gaishe ta, Mairo ta amsa cike da girmamawa, Saudat ta zauna gefen kujera muryarta a sanyaye. ta ce
“Momy fa?”
Mairo tace “Tana kicin tana. hada wa Alhaji abin karyawa, jiya ya dawo garin cikin
Dare Saudat ta kada mata kai tana saurarenta. ‘ . ” Mairo tace .“Me za a kawo miki Saudat?
Akwai kunun tsamiya da soyayyar doya da kwai, kuma akwai ,farfesun kifi, akwai ruwan tea idan kuma da akwai abin da ki keso sai ki fada a kawo miki”. ‘ ’Saudat ta ‘girgiza kai’ kafin tace
“‘A kawo min doya da kunun‘ tsamiyar
Mairo ta amsa da, “An gama”. Sannan ta juya ta nufi kicin, Saudat ta gyara zama ta jingina bayanta da makarin kujerar tana kallon qatuwar talabijin din dake makale a bango tana ta qaraji ita ‘ kadai.
Dr. Mariya ta fito daga kicin ta nufo Saudat tana fadar. ‘ ’
“Wai har kin tashi kenan?”
Saudat tayi saurin yunkurawa tana gaishe da Mahaifiyar tata, Dr. Mariya ta amsa tana fadar
“Jiya da daddare Alhaji ya shigo gari ina kicin ina hada masa abin karyawa, ne na hada ‘ muku tare, nasan ai zaki so kici abincin momynki k0?“
‘ Saudat tayi dariya tana fadar. “Ina so mana”.
‘ _ Dr Mariya tace, ““Okey, give me just five minute only” , ‘ ‘”
, Ta juya da. hanZarinta ta bar Saudat na maimaita yaren da mahaifiyar tata tayi, wanda in
za a hadata da wuqa bata San abinda take nufi ba. ta maida hankalinta wurin ‘
kallonta.
. Kamshin sanyayyen turare ne ya daki ‘ hancinta, tayi saurin daga kai tana kallon mai shigowar, babban mutum ne wanda a kalla shekarunsa zasu haura hamsin da biyar baKi ne mai haske, dogo mai kyakkyawar fuska da dan
siririn sajensa iya kunne, doguwar jallabiya ce a jikinsa milk colour sabuwa dal mai hade da
hularta. ,Suna. hada ido da ,Saudat ya sakar mata ,wani lafiyayyen murmushi, Saudat taja jiki tana gaishe shi Ya amsa lokacin da yake zama saman kujerar dake fuskantarta muryarsa a sake ya ce.
“Saudat k0?”
Ta daga masa kai alamar eh. , Ya ce “Masha Allahu, matso nan mana Saudat, taso matso kusa dani ‘yata”.
Saudat taja Kafafuwanta ta matsa inda
yake, ya sa hannu ya dafa kanta yana fadar ’ ‘ “Nayi farin cikin ganinki sosai don dama
na yiwa Hajiya maganar zamu samu lokaci muje dubo’ «ku to ashe ma Allah zaiyi ikonSa
Alhaji Ashiru yace “Da dai yafi”; . kaji ‘yan boko ba a maganar islamiyya sai boko, boko, shin ko a gobe qiyama wace irin rawa bokonnan zatataka? ‘ Dr Mariya tace, “Muje ga abin karyawa can saman tebur”. Alhaji Ashiru ya mike yana kallon Saudat,” yace’ “Taso muje ‘yata mu karya”. Ba musu ta mike saboda yadda Dr Mariya .ta zuba mata. idanuwa, kai tsaye saman kujerun dinning table suka hau suka zauna, Dr Mariya ta zuzzuba musu komai a faranti, ta turawa kowa a gabansa. ne da kwai sai kwallon doya tare da soyayyen dankali, da soyayyar plaintain, ta ‘ hada wa kowa ruwan tea mai kauri ta tura masa, sai qamshin ’ citta yake ‘* » Saudat ta saki ciki tana cin abincin kamar yadda taga kowa nayi, jefi jefl har suka kammala Alhaji Ashiru ya mike yana fadar “Bari in shiga daga ciki na dan kwanta na
. huta, around 12 saiki tayar dani” .
Dr Mariya ta amsa da, “To”
Sannan ya juya ya shige ciki
~. Can Dr Mariya ta dago tana kallon Saudat
“Wai ya maganar Dr. Ahmad ne Saudat bana
ji kince ya aiko miki dawata takarda ba a lokacin da kika fada masa an daura miki aure ba?” ‘ Saudat ta amsa da, “Eh” .
Dr. Mariya tace“T0 ina ta ke?”
. Saudat tace“Tana cikin haBar rigata na kulle a kayan dana cire jiya”. . .
Dr. Mariya tace “Okay, tashi ki dauko min.
Saudat ta mike ta dauko mata takardar wadda taji dauri duk tayiyaushi Dr.Mariya ta karba. tana dubawa babu komai a saman takardar sai lumbar waya da suna. Dr. Mariya ta dauki wayarta wadda ke ajiye a saman tebur ta lallatsa lambar ta kara a kunne ta kira yakai sau uku amman ba,a daukaba ta tuno aimanya irinsa basa amsa kiran bakuwar number don haka tayi masa rubutaccen sako ta tura K0 minti biyar batayi da tura sakonba akakira Dr. Mariya ta danna’ amsakiran sannan tasa a kunnenta tare da fadar. ’ “Assalamu alaikum,‘ barka da wannan lokaci”. Cike da girmamawa Dr. Ahmad ya hau
gaisheta tamkar yana gabanta, Dr. Mariya ta amsa
ita ma cike da kulawa tace
’ ” ‘ “Sunana Dr. Mariya Sani, nice mahaifiyar Saudat nasan za kayi mamakin kiranka da nayi
. Dr Ahmad ya amsa. da, “Haka ne Momy, amma Allah yasa Saudat din lafiya take”””””
Ta dan yi murmushi kafin tace
“Sai godiya ga Allah,nakirane dama in maka godiya akan abin alkhairin da kayima Saudat, na gode kwarai Allah ya saka da alkhairi”.
Dr. Ahmad ya sauke ajiyar zuciya yana fadar
“Amin Momy, na gode kwarai wallahi, na kuma ji dadi daya kasance Saudat ta hadu da mahaifiyarta, wannan yana daga cikin burina a rayuwa, na gode wa Allah”.
Momy tace, “Babu komai nike da godiya, ga Saudat din”.
Ta miqa wa Saudat kan wayar ta ta mike tayi gaba abinta.
Saudat ta kara wayar a kunnenta, tare da sallama, lokacin da muryarta ta dira kunnen Dr. Ahmad sai daya zabura ya tashi zaune daga
kwanciyar da yake yana fadar.
“Saudat kece amin wa ‘alaikus salam, daman zan Kara Jin muryarki Saudat harna cire rai, .yaki ke ya maigidan?”
~’ Saudat ta danja numfashi kafin ta soma baShi labarin duk abubuwan da suka faru, Dr Ahmad ya sauke wani gwauron numfashi kafin yace
“Dama nasan hakan zata kasance Saudat
saboda dama can anyikine donni kadai ketawa ce Saudat ni naki ne insha Allahu, kuma zan tabbatar miki da hakan duk abinda. Nake yau sai nazo Katsina, kisaurare ni nanda qarfe biyar na yamma zaki gan ni gidanku. Bawa Momy wayar ta bani adreshin gidan”. ‘
Saudat ta amsa da, “To”.
Sanan ta mike ta nufi falon data ga ta shiga, qaton falo ne mai dauke da kayan alatu na jin dadin rayuwar duniya.
Tana zaune kan kujera da system a
Gabanta tana. danne-dannenta,‘ Saudat ta mika wa .
Momy wayar ta karBa ya sanar da ita zuwansa ta bashi adireshin gidan da lambar gidan, saunan ta mike ta nufi Bangaren Alhaji Ashiru ta sanar da shi .
Da kanta ta dauki mota ita da Saudat suka shiga kasuwa tayi siye-siye masu yawa na tsadaddun dogayen riguna, arebiyan dres Indiyan dires riga da siket masu tsadar gaske, sai ‘ data sai mata kusan kala shida *da tsadaddun ‘ takalma masu kyan gaske, sai kayan shafa da
turarruka masu kyau
, Daga nan suka wuce gidansu Shukura suka taho da ita saboda gobe zasu tafi qauye a tare, ta ‘dauko dan qaramin akwatinta suka taho. Ba qaramin dadi Saudat tajiba dasuka tahoda
Shukura. ‘ Karfe biyar saura Momy taga Saudat zaune
itada Shukura afalo anata hirar makarata momy ta ‘
zuba mata idanuwa kafin tace “Waike ba bako zakiyibane,bazaki tashi ki shirya ba?” Saudat tace, “Shiri kuma Momy? Ai a shirye nake Momy tace“Lallai,to mazaki tashi ki canza wani shirin yanzu kije ki watso ruwa, ke kuma Shukura ki zaba mata kayan da zata sanya, bari inje kicin’inga idansun kammala aikindana saka sasu”. Duka suka amsa da, “To Momy”. ~ Ta juya ta fita, Shukura ta dubi Saudat tana fadar. “Kebakicewa bako zaki kika wani tule a ‘nan?Ai wallahi danasani yauda baqo da harwurin gyaranjiki zamuda acanza ayimiki makeup Saudat ta waro ido tana fadar “Kai Shukura, me ya kai har da wani
Gyaran jiki?“
Shukuratace, “Aukebaki da labarike nan? Saudat yadda hadaddun maza wayayyu masu ajike tsada ai doletun kina agida saikinbi matakan mallake naki saurayin; ‘
‘ Tun daga kwalliya, daurin kallabi, sa kaya masu kyau, fesa turare mai kamshi, fesa mouth freshner saboda wurin magana. Kashe murya da yin lafuzza masu ma’ana da burgewa, iya jera kalaman soyayya cikin sassanyar murya, iya lallausan kallo cikin kwarewa da kissa, ‘yar zolaya ki zolaye shi cikin sigar wasada dan bashi dariya kadan a cikin hira da‘ yar shagwaBa cikin sigar jan hankali, da kuma kamun kai a matsayinki na yar
mutunci. Wannan sune kadan daga cikin abubuwan dake sawa budurwa ta mallake saurayi, wallahi Saudat da soyayya nake da an sha kallo”.
Saudat tayi murmushi kafin tace“To me , yasa ba kiyi?” ’
Shukura ta tabe baki, tace
“Wallahi Abba ne bai bari ba, amma duk da haka ina dan taBa wa sai dai a waya ne kawai, shi ‘ ma Ummi ba ta sani ba, nasan da taci ubana don , har: yanzu ban kammala digiri dina bafa” .
Saudat ta nufi kewaye tana fadar
~ . :‘Ke kima godema Allah kin samu an tsaya miki kinyi karatun”
-. Ta tuna ita nata ubanda kansa ya hana ta ‘ karatun yasa‘yar uwarta makaranta tun daga” firamare har sakandire, amma ita bai saka taba. ‘ .Ta lumshe idanuwanta a daidai lokacin data sakar wa kanta shawer
‘ » Bayan tagama wankan tafito tasamu har Shukura ta gama fidda mata kayan da zata saka,
wata hadaddiyar’ doguwar riga ce wadda aka yi wa adon jajayen fulawowi sannan aka jejjera kalakalan duwatsu a ciki, rigar ta yi masifar kyau irin mai kama mutum ce daga sama daga qasa ta bude sosai tana da dogayen hannuwa irin masu tsukewa daga qasa suma an qawata su da adon rigar, sai kallabin rigar, Shukura ta hada mata da wani takalmi fari mai dan tsinin dunduniya kadan.
Saudat ta zauna tana fadar.
“Ke kuma wannan ce ta burge ki?”
Shukura tace, “Ai ki sa ki gani ba qaramin kyau za tayi miki ba
‘ Saudat ta zauna bakin madubi tana murza mai a jikinta. . Shukura ta mike tana fadar. ‘ ‘
“Tsaya ki gani Saudat in miki makeup ” Ba musu Saudat ta zuba mata idanuwa kawai tana kallonta, kwalliya sosai tayi mata da
hodoji da air pencil, air liner, jan baki mascara da ‘ sauran kayan kwalliya.
Ita kanta Saudat tsaye tayi tana kallon kanta a madubi, ta waigo da fara a a fuskarta tana ‘ kallon Shukura tace
“Kai k0 dai kinje makarantari koyon
kwalliya ne? ai wannan k0 shago ba zasu nuna miki komai ba”. ‘
Shukura tayi dan’dariya kafin ta ce_
“Ke kuma kin hadu kamar sarauniyar qasar waje
Duka suka sa dariya, Saudat ta janyo kayan ‘ za tasa, Shukura ta ce
“Ke tsaya-tsaya”.
Ta dauko wani sabon turare irin mai laushinnan mai suna soft ta gogamata a dukkanin gabobin jikinta har: zuwa bayan kunne wuya, mara da qirji, sannan tace
“Sanya kayan”.
Tana sanyawa ta kawo turaren (the warior body Spray) ta bata ta fesa a can cikin jikinta,
sannan ta mika mata turaren x5 ta fesa wa ,kayanta, ta bata qananan ‘yan kunne ta makala’ a kunnenta, sannan ta gwada mata irin nadin da za tayi wa gyalen rigar irin na ‘yan matan jami’a, ita kanta Saudat din ta san tayi kyau na ban mamaki, don haka bata da bukatar wani ya Kara fada mata
Shukura ta janyo jakartata ciro mouth freshner mai qamshin water milon ta feffesa mata a baki
don Kamshi da dauke datti, ita kanta yau Saudat ba za tave ga kalar Kamshin da ta keba, tana cikin sa takalmin Dr‘ Mariya ta leko tana fadar.
‘ “KarBi ga waya ana kiranki”. ‘ Saude ta karba ita kuma ta juya tayi gaba abinta, Dr Ahmad yace
“Gani a qofar gidanku”.
Saudat tace “To minti biyu”, ‘
Ta kashe wayar tana kallon Shukura tace
Yar uwa gashi a waje”.
Shukura ta mike, “Bari inje in shigo miki da shi”.
Saudat tace “Yauwa”.
Shukura taja qaramin mayafinta ta dora saman kanta, sannan ta fice, tunda Dr. Ahmad ya. hango ta zuciyarsa ta ba shi ‘yar uwarta ce saboda yanayin jikinsu iri daya ne dogaye amma basu da kwari sosai, suna da doguwar fuska mai dauke da dogon hanci da dan siririn baki, don ita Shukura ma manyan’ idanuwa gare ta sosai masu kalar kyau, farare tas~ tas da su, don dai ita baqa ce amma irin bakinnan mai haske wato black beauty kenan, sabanin Saudat dake jajawur kamar a taBa jini ya’ fito.
Shukura ta hango wata tsadaddiyar mota
‘ mai kyan gaske, sabuwa dal mai kala da yanayin jirgin sama. Shukura taja. ta tsaya don bata taBa
“ganin irin motar ba tunda take a duniya, gashi farar motar mai bakin gilashi ce, baka iya ganin * Wanda ke ciki
Da hanzari ta ga an bude qofar motar kujera mai zaman banza, wasu mutane su biyu suka fito da hanzarinsu suka bude gidan baya na motar. ” ‘
. A hankali yasA qafarsa guda ta fito
Qasa sosai, sannan ya sauko da gudar ya fito gaba daya. Shukura ta zuba masa idanuwanta kyakkyawa ne na qarshe, abin da zuciyarta ta fada kenan, ta nufe shi da nutsuwarta tana fadar. “Sannu da zuwa, ba zaka shigo daga ciki ba?” ’ . Dr. Ahmad ya girgiza mata kai kafin yace. “Mitar tana da girma ne sosai ba kowace haraba bace za ta isa a yi kwana da ita a ciki ba, muje kawai”.
Shukura ta yi gaba, ya rufa mata baya har cikin qawataccen falon, tayi masa masauki sannan ta wuce kicin tayi wa Momy magana ta nufi daki ta kirawo Saudat wadda ta yi zaune gaban madubi ta zuba tagumi da hannuwa bibbiyu tana kallon kanta, amma a zahiri zuciyarta ta lula duniyar Dr. Ahmad wai yau gani ta ke abubuwan ‘ suna faruwane kamar a cikin mafarki, wai yau ita ce za su hadu da Dr. Ahmad a matsayin masoya
bata san lokaCin da tayi wani murmuShi ba, Shukura ta tsaya daga gefenta tana fadar ‘ ‘ ’ “To saiki tashi yana falo”.
Saudat taji wani irin yarr a jikinta, ta ta miqeta nufi kofa har: zata fita ta juyo tana kallon Shukura ta ce
“Don Allah ki zo ku gaisa”.
Shukura tace, “Ki fara zuwa ina tafe
Ba ta sake magana ba ta juya tafice ta same shi a hakince saman daya daga cikin kujerun dake falon, yana latse~latse a wayarsa. Tana shigowa kamshin turarenta ya daki hancinsa, ya dago da sauri yana kallon mai tahowar, suka yi ido hudu.
‘ Saudat tayi wani murmushi ta juya da sauri
ta nufi faloun Momy ta fada mata tana nada kallabin jallabiya a kanta, Saudat tace
“Momy gashi yazo
Tace“Kije yanzu zamu fito da Alhaji sai mu gaisa_
Saudat ta juya tayi gaba
A tsaye ta iske shi a yanzu, ya zuba ‘_ hannaye cikin aljihunsa, Saudat ta Karasa har inda ‘ yake ta zube saman gwiwoyinta tana fadar. ” ”
‘ “Sannu da zuwa Yallabai, barka da zuwa ina wuni
Dr Ahmad ya zuba mata kyawawan » idonsa masu kamar an diga gold yace.
Shine kin fito kika koma don kija min ‘rai saboda kin sani sarai ina cikin qishirwar son ganinki k0? Allah yadda na mike din nan na rantse da sai dai ki gan ni bayanki”
Ya bude hannayensa
“Taho gareni don Allah Saudat’
; Saudat tayi saurin rufe bakinta tana dariya, Dr. Ahmad ya zauna ya tattara nutsuwarsa a kanta,
kafin ya ce
“Saudat kin qara kyau wallahi kamar ba keba,irin wannan kamshi haka aisaikija intare a nan” .
Murmushi kawai tayi, Dr. Ahmad ya gyara zama kafin ya ce
“Wallahi Saudat farin cikina a yau ba zai misaltu ba, duk yadda zan kwatanta miki ba zaki gane ba, don Allah ina Momy dinmu in sata cikin idanuwana ko naji sanyi, wallahi ba kiji dana ji muryartaba sai na ji kamar da Mom dina nake magana, wallahi naji ina qaunarta nima”.
Saudat tayi murmushi tana amsa sallamar Momy wadda suka shigo cikin falon, Alhaji Ashiru ya amsa.
“A‘a wa nake gani yau a gidan namu, wai.
Ahmad kai ne da kanka?” Dr Ahmad ya zabura ya miqe tare da washe baki yana fadar ‘
Lah wai Daddy dama nan ne gidanka na Katsinan ashe?” Alhaji Ashiru ya ce“Ai k0 dai nan ne ai shi Alhajinka ya sani, don har ya taBa zuwa Dr Ahmad ya ce, “Ikon Allah ashe gidan
Daddyna nazo . ~ Ya durqusa yana gaishe su, duka dadi ya
cika su don haka cikin fara‘ a suke amsawa.
Alhaji Ashiru ya juya yana kallon Dr Mariya yace
“To ai ke wannan tuwona maina ke nan, wannan dan Yaya Alhaji ne babban wanmu wanda , aka yi wa aure tun last four years, bai taBa zuwa‘ gidan nan ba tunda muka yi aure, kullum in nayi magana sai yace kishi yake taya Hajiya, to yau ga
‘ shi har cikin falonki tasa ta kawo shi, don haka kema saiki Juya kambunki”. ‘
Dr. Ahmad yana murmushi yace.
“Lah wallahi kawu ba haka bane kasan abubuwan ne sai a hankali, amma dai tuba nake ai yanzu zan rinqa zuwa” . .
Dr Mariya tace “Ai dama :zaka rinka . zuwa mana tunda yanzu taka ta kawo ka” .
‘ Duka suka sa dariya ban da Saudat wadda tunda ta sunkuyar da kanta bata kara dagowa ba,
. sai ta koma ita ce sarakuwar. su kuwa hira ce sosai “suka Barke har Shukura ta shigo aka dasa da ita, sai
lokacin ne Saudat ke dan sa baki kadan~kadan har
sai da aka kira sallah, sannan suka fice suka tafi . don sauke farali. Suna dawowa Momy tasa Mairo
ta kawo abinci aka dasa wata hirar a nan suka”
tsaida ranar zuwa qauye sati mai zuwa don tsaida , maganar auren.
Dr. Ahmad bai bar gidan ba, sai qarfe goma na dare, Saudat tayo masa rakiya har bakin gate, ’ya tsaya yana kallonta muryarsa a sanyaye yace
“Yau zan yi bacci har da munshari Saudat na tabbatar a wannan karon zan mallaki abin da zuciyata keso, lallai na yarda babu abin daya fi qarfin Ubangiji k0 ba haka ba my dear”; ,
Saudat dake faman wasa da ‘yan yatsun hannunta tayi murmushi kawai ba tare da ta tanka masa ba, Dr. Ahmad ya bita da kallo gabadaya idanuwanta na saman yatsun hannu nata, ya miqa hannunsa ya riko duka hannayen ya janyo ‘ ta gabansa.
Da sauri ta waro idanuwa tana kallonsa, ya sakar mata murmushi tare da hure mata idanuwa’ da sauri ta idanuwanta tana murmushi qasa-qasa “ ‘ yace.“Ki bari sai kin koma gida kin kwanta sannan ki bude kinji?
’’ Ta daga masa kai alamar ta yarda sannan . ya. sakar mata wani siririn murmushi kafin yace
‘Saida safe, ki kular min da
kanki, bacci mai dadi”. . Ya shafi kanta daidai lokacin da take
Qokarin juyawa don haka ta qara sauri yana kallonta harta bace ya sauke wata nannauyar‘ ajikyar zuciya sannan ya juya ya fice. _ .Bacci ya kaurace wa idanuwan Saudat, jinta ta‘ ke tamkar’ ta taka rawar murna duk ta damu Shukura da juye~juye, sai faman juya takardar da ‘yasa mata ahannunta take koda batasan meye ya rubuce ba, amma ta san cheque ne na banki, don
haka yau zuciyarta fes ta kwanta. Tun da gari ya waye suka hau shirin tafiya
Qauye, Shukura ta shirya cikin wasu riga da siket na wani swiss‘ lace mai shegen kyau da tsada, dinkin yabi jikinta ya hau kalar fatarta kasancewar leshin light blue mai adonda “ruwan qasa-kasa, gashin nan ya sha gyara an daure shi a gefen kunne sannan ta nada daurin kallabinta mai suna touch Iight irin na ‘yan matan yanzu. . Gyalenta da takalminta duk farare ne, sai
‘dankunne da sarka na gwal tare da abin hannunsa ta yi kyau sosai kasancewarta dama . kyakkyawarce ajin farko ’ Saudat kuwa riga da siket ne ta saka dark
brown mai adon yardin gwal a jik; irin na Indiya
.ta gyafa gashin kanta ta daure shi a baya ta saki jelarsa’ a gadon bayanta sannan ta nada gyalen _ kayan saman kanta ta sake shi bai rufe kwallliyar kayan ba, siririn dankunnenta na gwal da abin ‘ hannu wanda mahaifiyar Dr.ta bata Tasa ba tasa abin wuyan ba saboda rigar kayan ta rufe har wuyanta ta kawo takalminta golden mai tsinin dunduniya ba qaramin kyau ta yi ba, yar’ indiya sak!
Sannan suka fito falo inda Momy da Alhaji ke jiransu, Saudat tabi Momynta da kallo wadda ke sanye da riga da siket na atamfa sai ta dora ‘ baqar doguwar riga a sama mai adon jajayen fulawoyi irin mai tsukakken hannun nan ce
Ta‘ daura kallabin atamfar a kanta sannan ta dora kallabin rigar a kan nata, ta saka takalmi da jaka jajaye, hannunta da kunnenta da wuyanta ma gwal ne mai tsadar gaske. Haka su Nabil da Nabila sun hade cikin ‘yan kanti kamar ~ ‘ ba” yan Nageria ba. ’ .
‘ Dadi ya cilka Saudat, wai nan duk yan uwanta ne da mahaifiyarta, wayyo rayuwa ke nan, sai da suka gaisa da Momy da Alhaji sannan ta bawa Momy cheque din da
Dr Ahmad ya bata Momy ta warware tana dubawa tare da zare ido, tace
“Kai wannan kudin Sunyi “yawa is too much, yayi yawa abin duba ka gani Alhaji five ,
Hundred thousand fa”.
‘ Alhaji yace “Ta gode kwarai ai kyautar soyayya bata yawa; ki bude mata account kawai ki zuba mata a ciki
. Hajiya ta amsa da, “To”. Sannan suka mike suka nufi tebur suka karya gabadaya sannan suka fice suka shiga wata Katuwar
motar Alhaji suka tafi humer jeep baka mai kyan gaske, shi ya ja su da kansa, har zuwa cikin Dandagoro. Jefi-jefi akan taBa hira inda Saudat saurarensu kawai take, amma zuciyarta ’ ta shiga duniyar tumani da sake-sake ganin al’amuran take tamkar a cikin mafarkinta suke ,
Faruwa jira kawai take ta farka a kowane lokaci_ba.
. ‘ALHAMDU LILLAHI Masha Allah.
Mu hadu a littafl na HUDU kuma na karshe ldan mai kowa mai komaI ya kaimu
NAKU HAR KULUM
*ABDULLAHI ISMAIL SALANKE*
TABA KA LASHE
kadan daga cikin yar tallah book4
Dukkansu suka fito suka shiga gidan saudat na riqe da hannun nabiLa shikura na gefenta sai nabil a gefen momy alhaji ashiru ya zauna yana jiransu a mota sallamar da sukene ta janyo hankalin inna laure dake kuryar daki tana tattara komatsai tayo tsakar gidan tana fadar marabanku sannunku dai
Turus taja ta tsaya gamida dafe kirji cikin tashin hankali da kyarmar murya ta soma magana su waye ku daga ina?
Momy ta gyara tsayuwa gamida cewa ikon Allah abin da mamaki idanni baki ganeniba ai ina tunanin wannan yarkice kya ganeta tayi maganar tana nuna saude inna laure ta fadi qasa jabar kamar an tile kayan wanki tana kwalama malam bala kira malam bala ya fito daga kewaye a gigice hannunsa riqe da buta yana fadin kai laure wannan irin ihu haka ai saikisa juwa ta kwasheni in fadi babu gaira babu dalili
Inna laure ta dinga nuna masa momy tana fadin malam dubamin ka gani wacece nake gani kamar maria
Cikin firgici malam bala ya siki butar ta fadi facal yayo kansu yana fadin wacce mariyar kike nufi
Hmmmm lol ya abin yakene Mu tara gobe