ZEENAT YAR JARIDAH CHAPTER 13
ZEENAT YAR JARIDA
CHAPTER 13
Zatace Ina Ahmad din kenan sai gashi ya shugo da sallama, Samun kujerar dake dakin yayi ya zauna sannan ya gaishe da Maman da jiki Tace” Jiki Alhamdulillah nasama sauki ba abun dake damuna yanzu, Alhamdulillah yace Mama tace” ya akai da fatan dai an sama nasara naga kun Dade Zeenat ta sace kallon Ahmad taga Yana wani murmushi
Ahmad kuwa yace” Allah ne kawai ya rufa Mana asiri da yau sedai kiji wani labari
Mama ta Dan zare ldo tace” bangane ba, Nan suka Bata labarin from A to Z
Tace” kaji marajin yaro da karfin Hali, yanzu ai gashinan ya janyo ma kanshi abun dayafl karfinshi, Zeenat tace” wlhi kuwa, mama tace” Allah ya tsare sukace Ameen
,,,,,,,,,
Bayan kwana biyu Soyayya me karfl ta shiga tsakanin Zeenat da Ahmad, An Sallamo mahaiflyarta gaba daya sun dawo gida! Mama tai ma Ahmad godiya sosai yace” bakomai
Mahaifiyar Mudansir kuwa se up and down takeyi Dan ta samu Mudansir ya fito Amma abun yafi karfinta Dan an shaida mata abubuwa da ya Dade Yana aikatawa, Tayi kuka sosai Da danasanin rashin tsawata mai da tai tun farko….
Tunda Zeenat ta dawo wajen mahaifiyarta, taji komai yadawo mata Sabo, Yanzu hankalinta kwance ba abun dake damunta, Tana flta aikinta ta dawo komai normal, bangaren abinci kuwa se Wanda Sukeso Dan Ahmad ya ciki yana masu store da abinci kala kala, yanzu suna rayuwa me Dadi, cikin Yan kwanaki kadan Zeenat tayi kyau Domin har Yar kumatu tayi..
Yau kwanan Ahmad uku besa Zeenat a Ido ba se dai kullun suna cikin waya, Saboda Bata Zama sosai, yau weekend yasan Tana gida Wanka yayi yasa red shirt da wando, ya fesa turere me sanyin kamshi, ya dauka key yayi gidan su Zeenat
Yana zuwa ya aika wani yaro yaje ya kiramai ita Tana Zaune Tanajin redio saiga Wani yaro ya shugo wai ana kiranta,
Cema yaron tayi je kace ganinan zuwa Dan tasan dama Ahmad ne, Daki ta shiga ta dakko Dan karamin gyalen abayar Rigan jikinta tace ma ummanta Ina zuwa, Tace 0k sai kindawo Tagaida shi Fitowa tayi ahankali Tana tafiya kamarwacce kwai ta fashe mawa a ciki
Kollonta yayi tacikin mota Yaji Sonta na Kara shigarshi, gaskiya yayi dacen mata komai nata a natse take yinshi sai ma kun ganta Bude kofar motar tayi ta shugo ta gaisheshi kanta a kasa Tana wasa da Yan yatsunta dogaye, shina kallon yatsun yayi yaga sun burgeshi yace” Wow Sauri tayi ta boye hannunta ita har Yanzu kunyarshi takeji Zeenat yace“ cikin wani irin muryan da ya saukar mata da kasala Nan take Look at my eyes yace” tai Shuru yazo daidai kunnata yace” I love you my baby, I miss you, You’ll be mine forever “Ita dai hmm kawai tace” Wani nunfashi yaja da seda ta kalleshi, taga ya chanza, iya saninta da Ahmad be shaye
Shaye bare tace ko yasha wani Abu ne, Kara kallonshi tayi for the 2nd time tace” Baby are you okay kuwa? Bazaki gane ba yace” ranar dai rasa kanshi tayi tace” to me ke damunshi sun Dan taba Hira kadan, sannan yace” please gobe Sunday in ba damuwa ki sanar wa umma gobe zanzo na dauke ku kuje Gidan kanana dasu Inna wuro Wow tace” are you serious? Yace yes dear, Kinga muna dawowa sai ai auramu, shuru tayi Tana nazarin Aure? Tana
Tunanin Zuci batasan Sanda ya fito ba tace” Aure ni da ban tara komai ba
Ashe Yaji, Yace” don’t Worry Komai ni zan miki, taji kunya ta rufe ido ta fito da sauri tai cikin Gida, ya kalleta yace” my shy shy girl frnd, sannan ya tada Motar yai gidan Kabir Yana zuwa Suka gaisa Nan ya sanar dashi gobe yanaso ya rakashi kauyensu, Kuma tare da sirika ce bazaiji dadin tafiya shi kadai ba, Kabir yace” Allah ya kaimu, Ahmad Wai yaushe ne auran naku?
Ahmad yace” muna dawowa bazaiyi taking time ba, Kabirr Yace Ah ah kaga Ango mijin amarya Itama Zeenat Tana shiga ta sanar da mamanta akan gobe su shirya ze kaisu Chan inda su ka tsinceta Maman tace” Alhamdulillah dama inataso lnje inga Yan albarkan na Zeenat tace” wlhi Kuwa
Da darene Suna Zaune da Mamma dinta Suna Hira phone dinta ne yai ringing Tana dubawa taga _beloved_ smiling tayi ta fIta a dakin Dan kunyar mamanta takeji sosai
Tana futowa wayar ya katse Dan tsaki tayi Dan tasan is hardly ya Kira Dan ya Kira Sau daya be sametaba kyaleta yakeyi Dan kar ya takura mata Samun waje tai ta zauna, Tana cikin Tinaninshi taji phone din ya sake ringing ga mamakinta Tana dubawa taga shine, Wow tace sannan tai picking, Ahmad yace” Hello baby nah Tace” mesanyina how are you doing? Yace” m doing great n you? Tace” same here, Kowa shuru yayi sannan yace” inata missing dinki sosai fa, Wani lumshe
Ido tayi kamar Tana ganinshi tace” bakai kadai ba Yace” talk true bayan ko mun hadu sai ki tajin kunya, tace” kar ka damu, Nidai nasan ina missing Dinka, Nan dai hirar Soyayya suka Sha sosai da dukkaninsu sai da sukaji inama tare suke! Balle ma Ahmad aranshi yace” Dana gwada Miki son da nake maki, Sun Dau
kusan awa daya Suna Hira sannan sukai sallama Ahmad Suna Gama waya wani rufe ido yayi yasa wayar a kirjinshi tare da wata numfashi…Ita Kuma Zeenat Suna gamawa daki ta shige Sadaf Sadaf tai Sa’a mamanta tai bacci dama batason waya Mai tsaho Dan haka itama ta samu waje ta kwanta Tana hango rayuwar da zasuyi da Ahmad ‘Washe gari’
Call din Ahmad ya tasheta, Batai picking ba Duba wayar tai raga 6:30 da sauri ta tashe mamanta tace” ki tashi muyi salla yau mun makara Bayan sunyi salla sun kammala komai na gidan suka Fara shiri, sun kintsa Ahmad din suke jira
Bangaren Ahmad kuwa tun asuba ya farka yai wanka ya shirya bawai matsuwar zuwa kauyen yasa yake dauki ba aa tsabagen Son ganin sanyin idaniyanshi yake
Around 9 yai parking kofar gidan su Kabir ya daukeshi suka wuce gidan su Zeenat, ahanyane yake sanar Dashi son da yake ma Zeenat a jinin jikinshi yake, Kabir yace” Naga alama lokaci daya so yama kamu ka tashi daga Ahmad ka dawo Amadudu, Dukansu dariya sukai
Kabiryace” Yausheni bikin wai ya kamata musan abunyi, Ahmad yai murmushi Yana murda kan sitiyarin mota yace” Nan da One Week nakeso, Kabirya zare Ido yace sarkin zalama one week fa kace?
Ahmad yace” yeah toh me zamu jira? Kabirya jinjina Kai yace” lalla abokina da gaske kake, Allah ya kaimu Ahmad yace” Ameen Taflya kadan sukai se gasu a Kofar gidan su Zeenat Nan suka fitO suka shiga suka gaisar da umman Zeenat, duk Abun da yake Zeenat Bata bari sun hada ldo ba, Dan wani nauyinshi takeji, Ahmad kuwa Yana lura da ita a ranshi yace” Zaki shugo hannu neh Baby
°°°°
Fitowa sukai gaba dayansu umma ta rufe kofargidan su Kuma Suna gaba, Ahmad ne yace” baby morning, Ko kallonshi Batai ba Dan tasan Tana amsawa ze iya kashe mata jiki da kallonshi, ga ummanta Kuma that’s why ta shareshi, Tafiya suke, ummanta duk a takure take Dan taflya da siriki sai dole, Suma kansu gaba daya a takure suke Dan ba wata Hira da akeyi dan haka Ahmad ya kunna redio Kowa ya maida hankalinshi Yana saurare,
Ahmad kuwa se kallon Zeenat yakeyi ta mirrow, ko Allah zaisa su hada Ido, da ta fahimci haka setaki kallo ta dakko wayar Tama ta Fara danne danne ta shige WhatsApp
Tana shiga taci karo da book din ‘ Nan tai concentrating akai sosai Dan book din ya hadu iya haduwa,
Ahmad Yaso yasan Me Takeyi Amma Ina ba Hali ganin Sun sauka kauyen Alhamdulillah, An musu tarba nazo a gani duk da kauye ne, Amma komai Kam Masha Allah, Dan fura da no-no seda suka ture, sun taba Hira sosai, Inna wuro
ta shaida ma mamanta Irinjin dadin zaman da sukai da Zeenat, mamanta tace” Allah sarki,
Inna wuro ta Kara da cewa da ace Bata da Kowa ne Nan Zata zauna, Kakan Ahmad tace” ai ko sunyi aure Nan za’a kawota ta zauna da mu, Inna wuro ta kwashe da dariya tace” ba’ayi haka ba
Nan Ahmad ya sanar musu da cewa sati me zuwa za’ai bikinsu, Abun ya musu Dadi sosai, ana haka Sega baba mijin Inna wuro, sun gaisa da mamanta Nan ma ya Kara cewa yason
Zeenat sosai, Basu taba haihuwaba jinta yake tamkar shi ya haifeta, Mamanta taji Dadi sosai, tace“ ai yanzu an Zama Yan uwa, Ana tare
Zuwan Nan ma datai seda ta gyara musu gida ta tattaro Yan wankinsu tayi, baba fulani har da kwalla wai haka kullun take Mana munajin Dadi
Sun taba Hira sosai, kamar kar su rabu, saboda Zeenat ta ta shaku dasu sosai Zasu tafine baba yace” a cikin shanayansa ya Bata guda biyu, duk lokacin da suka shirya suzo su amsa Sunji Dadi gaba dayansu, Zeenat har da kuka wai bataso taflya ba, Kabir ya Fara fltowa yai wajen mota Sannan ita da Ahmad suka fltowa, yazo daidai kunnenta yace” tunda kinason Nan idan munyi aure se in kawoki ki zamanki anan, Turo Baki tayi ta harareshi batasan Sanda tace“ Su nake aure ko Kai , Wani murmushi yayi yai mata gwalo yayo gaba ya shiga mota, Sannan mama ta fito ta rukota tace” Dena kukan Mana se kace yarinya Nan sukayo mota sai gida
Sun sauka gida Laflya Lau Alhamdulillah
,,,,,,,,,
washe gari maman Zeenat din ta shiga Makota Wanda suke Shiri da Yan uwan da baza’a rasa ba ta
sanar musu zeenat zatai aure, sunyi farin ciki sosai sukace Allah yakaimu lokacin