ZEENAT YAR JARIDAH CHAPTER 4

ZEENAT YAR JARIDA
CHAPTER 4
Zeenat tanata hada hadar harhada takardu a office dinta taji wayarta na ruri batabi takan wayarba don ta duba taga bakuwar nambace kuma saurinta takoma gida tayi wasu ayyukan agidan 
Gashi yau tawuce lokacin aikinta don shida takusa kuma biyar ne lokutan tashinsu akullum 
Fitowarta kenan titi tana jiran abin hawa taji ansake kiranta da bakuwar nambar nan ta dauka da sallamarta 
Abin mamaki saitaji ana kyalkyacewa da wata muguwar dariya kuma ba dariyar mutum daya bace ba 
Saita kashe kawai tana jan tsaki don gani tayi aikamar ma raina mata hankali ake 
Ta tare wani dan sahu tagaya masa unguwarsu da xaikaita tace masa ga yanda take biya take yace tahau kawai 
Tahau tana ganin kirkinsa domin wasu dayawa tirje mata suke inyamma tayi dayawa harsaita kara musu kudi akan yanda take biya kana suke kaita 
Suna cikin tafiya taga again kiran mutanen nan bata dagaba ta kyale harta tsinke akaita kira kusan biyar can da suka gaji saiga sako kamar haka 
_Zeenatu ikon Allah mace me kamar maza me taimakawa wadanda aka cuta yau munga hotonki kinyi kyau kinyimin dafatan nima inkika ganni ayau xan miki domin kina gab da isowa gun angon naki amaryata na aiko motar daukar amarya ta daukeki dafatan kinyi sallama da gida?_ 
Ta karanta wannan firgitaccen sako yafi sau uku gabanta taji yana faduwa take tahau addu,a cikin ranta 
to wannan wane shaidani ne haka? 
Da alama yayine domin ya tsorata ta dakyar ta samo nutsuwar ajikinta ta rubuta masa short message kamar haka _Ta Allah ba takaba wawa mahaukaci kawai_ 
da sakon yashigo wayar kwamanda bushewa yayi da wata mahaukaciyar dariya ya dubi Ashiru lauya yace “kalli abinda ta turomin lallai yarinya xakiyi dana sanin wannan kalami naki ayau saikin zama 
matar wawa mahaukaci arayuwarki 
Ya mikawa lauya ashiru wayar shima daya karanta dariyar yayi yace ” kaga kada ka aikata mata fasadi domin mudansir yace kada acutar da ita harsai in 
tabada camera din. 
Dariya kawai kwamanda yasaki tareda karbe 
wayarsa ahannun lauyan 
Lauya ashiru ya mike da sauri yace “bari natafi kafin akawota mayi waya latter inji yanda ake ciki. 
Kwamanda yace ” to hakan yayi inkaje kayi kokarin hadamu  da oga mudanssir. 
‘**** ****** *
Tunda zeenatu ta ajiye wayarta ajaka bayan ta tura sako xuwa bakuwar namba bata sake sanin inda kanta yakeba domin kauce hanya yayi me dan sahun nata yaron kwamanda ne shine dan aiken 
Yasauka ahanya yaringa kwararar gudu ba tsayawa Taga ya canxa hanya ammafa takasa bude bakin tayi magana domin wani ruwa ya fesa mata akwalba 
Sun dauki kusan awa biyu ahanya har duhu yakawo kai 
Don sai bayan magriba suka isa kasurgumin dajin 
Da suka shiga gidan kuwa binsa kawai take abaya yana kutsawa lungunan da ita zungui zungui take binsa badamar musu balle tirjiya 
Sun dau mintina kana suka isa chamber dinsu kwamanda 
Zazzafa sunan wanda yakawota ya gurfanar da ita gaban kwamanda 
Kwamanda yahau tafa masa yana fadin aikinka yana kyau zazzaafa babu abinda xai gagareka afadin duniyar nan kaga dan gaban goshin kwamanda Yakalli jama,ar dake gun sunyi goma yace dasu 
” kusheda daga yau anyiwa zazzafa karin albashi 
asakamakon wannan kokarin dayayi. Nan suka hau tafawa suna sowar murna Zazzafa ya rissina yana godiya Kwamanda yace ” ina sarkin gida? 
Da sauri wani d ‘an shawalwali mara jiki yafito yarisina yace ” gani ranka yadade adade anayi ayi karko. 
Kwamanda ya murmusa yace ” sarkin gida ga ajiyata nan akaita dakin dayafi kowanne kyau da girma domin ta wataya aciki karinga kula da duk wani motsinta duk randa ta gudu daga gidan nan to 
abakin ranka 
Sarkin gida yace “bama zata iya gudu a gidan nan ba ranka ya dade wace ita tagane hanya ai tashigo kenan. 
Kwamanda ya dubi wani dan gajere mummuna yace dashi ” sarkin girki ashirya mata lafiyayyen 
abinci inta dawo hayyacinta kada abata abinci irin
na kowa ita din ta daban ce kada ta nemi ruwa amakare akawo mata komi kafin ta bukata inka kuskure abakin aikinka ‘ 
Sarkin girki ya risuna yace ” angama ranka ya dade zankiyaye. 
Kwamanda yace “kada wanda yai mata bincike ajakarta harsai inta dawo hayyacinta ta bamu camera tukunna 
Suka amsa da ” to oga!! Ya umarci zeenatu data tashi tabi sarkin daki Ba musu ta mike dama arunkufe take agabansa 
Cikin bin umarni taringa binsa hardakinta me lamba 10 aka bude mata tashiga kawai Dayake hijab ne ajikinta kusan har guiwa jakarta na sakale akafadarta ta zauna akan kafet din dake 
malale adakin 
 rufe dakin yayi da kwado yajuya yatafi abinsa…. 
Hmm

Leave a Reply

Back to top button

You cannot copy content of this page

Adblock Detected

YOU ARE USING ADBLOCK TURN IT OFF TO COUNTIUE BROWSING OUR WEBSITE